Surata: Suratul Furqan

O versículo : 21

۞وَقَالَ ٱلَّذِينَ لَا يَرۡجُونَ لِقَآءَنَا لَوۡلَآ أُنزِلَ عَلَيۡنَا ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ أَوۡ نَرَىٰ رَبَّنَاۗ لَقَدِ ٱسۡتَكۡبَرُواْ فِيٓ أَنفُسِهِمۡ وَعَتَوۡ عُتُوّٗا كَبِيرٗا

Waxanda kuma ba sa tsammanin haxuwa da Mu suka ce: “Me ya hana a saukar mana da mala’iku ko kuma mu ga Ubangijinmu?” Haqiqa lalle sun yi girman kai don (suna) ji da kawunansu, suka kuma yi tsaurin kai babba qwarai da gaske



Surata: Suratul Furqan

O versículo : 22

يَوۡمَ يَرَوۡنَ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةَ لَا بُشۡرَىٰ يَوۡمَئِذٖ لِّلۡمُجۡرِمِينَ وَيَقُولُونَ حِجۡرٗا مَّحۡجُورٗا

Ranar da za su ga mala’iku[1] a wannan ranar babu wani farin ciki ga masu laifi, za kuma su riqa cewa: “(Albishir daga Allah) haramun ne abin haramtawa ne (a gare su)”


1- Watau ranar mutuwarsu ko a cikin qaburburansu da ranar da za a kora su domin yi musu hisabi.


Surata: Suratul Furqan

O versículo : 23

وَقَدِمۡنَآ إِلَىٰ مَا عَمِلُواْ مِنۡ عَمَلٖ فَجَعَلۡنَٰهُ هَبَآءٗ مَّنثُورًا

Muka kuma gabato zuwa ga duk wani aiki da suka yi, sai Muka mai da shi qura abar xaixaitawa



Surata: Suratul Furqan

O versículo : 24

أَصۡحَٰبُ ٱلۡجَنَّةِ يَوۡمَئِذٍ خَيۡرٞ مُّسۡتَقَرّٗا وَأَحۡسَنُ مَقِيلٗا

‘Yan Aljanna a wannan ranar su suka fi kyakkyawan mazauni kuma suka fi kyawon wurin barcin qailula[1]


1- Domin za a gama hisabi gabanin lokacin azahar, har ‘yan Aljanna za su shige ta su riski lokacin qailula a cikinta.


Surata: Suratul Furqan

O versículo : 25

وَيَوۡمَ تَشَقَّقُ ٱلسَّمَآءُ بِٱلۡغَمَٰمِ وَنُزِّلَ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ تَنزِيلًا

Kuma (ka tuna) ranar da sama za ta kekkece da girgije, kuma a saukar da mala’iku gungu-gungu



Surata: Suratul Furqan

O versículo : 26

ٱلۡمُلۡكُ يَوۡمَئِذٍ ٱلۡحَقُّ لِلرَّحۡمَٰنِۚ وَكَانَ يَوۡمًا عَلَى ٱلۡكَٰفِرِينَ عَسِيرٗا

Mulki tabbatacce a wannan ranar na (Allah) Mai rahama ne. Kuma ta kasance rana ce mawuyaciya ga kafurai



Surata: Suratul Furqan

O versículo : 27

وَيَوۡمَ يَعَضُّ ٱلظَّالِمُ عَلَىٰ يَدَيۡهِ يَقُولُ يَٰلَيۡتَنِي ٱتَّخَذۡتُ مَعَ ٱلرَّسُولِ سَبِيلٗا

(Ka tuna) kuma ranar da azzalumi zai riqa cizon yatsunsa yana cewa: “Ina ma na bi hanya tare da Manzo!



Surata: Suratul Furqan

O versículo : 28

يَٰوَيۡلَتَىٰ لَيۡتَنِي لَمۡ أَتَّخِذۡ فُلَانًا خَلِيلٗا

“Kaicona ina ma da ban riqi wane aboki ba!



Surata: Suratul Furqan

O versículo : 29

لَّقَدۡ أَضَلَّنِي عَنِ ٱلذِّكۡرِ بَعۡدَ إِذۡ جَآءَنِيۗ وَكَانَ ٱلشَّيۡطَٰنُ لِلۡإِنسَٰنِ خَذُولٗا

“Haqiqa ya vatar da ni daga bin Alqur’ani, bayan ya zo mini.” Shaixan kuwa ya kasance mai tavar da mutum ne



Surata: Suratul Furqan

O versículo : 30

وَقَالَ ٱلرَّسُولُ يَٰرَبِّ إِنَّ قَوۡمِي ٱتَّخَذُواْ هَٰذَا ٱلۡقُرۡءَانَ مَهۡجُورٗا

Manzo kuma ya ce: “Ya Ubangijina, lalle mutanena sun riqi wannan Alqur’ani abin qaurace wa[1].”


1- Watau ta hanyar guje wa sauraron sa da rashin karanta shi da aiki da koyarwarsa.


Surata: Suratul Furqan

O versículo : 31

وَكَذَٰلِكَ جَعَلۡنَا لِكُلِّ نَبِيٍّ عَدُوّٗا مِّنَ ٱلۡمُجۡرِمِينَۗ وَكَفَىٰ بِرَبِّكَ هَادِيٗا وَنَصِيرٗا

Kamar haka Muka sanya wa kowanne annabi abokan gaba daga masu laifi, kuma Ubangijinka Ya ishe ka Mai shiryarwa Mai taimako



Surata: Suratul Furqan

O versículo : 32

وَقَالَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ لَوۡلَا نُزِّلَ عَلَيۡهِ ٱلۡقُرۡءَانُ جُمۡلَةٗ وَٰحِدَةٗۚ كَذَٰلِكَ لِنُثَبِّتَ بِهِۦ فُؤَادَكَۖ وَرَتَّلۡنَٰهُ تَرۡتِيلٗا

Waxanda kuma suka kafirta suka ce: “Me ya hana a saukar masa da Alqur’ani gaba xaya, a lokaci guda[1]?” Kamar haka ne (Muke saukar da shi kaxan-kaxan) don Mu tabbatar da zuciyarka da shi, Muka kuma karantar (da kai) shi daki-daki


1- Watau kamar yadda aka saukar da littafin Attaura ko Linjila.


Surata: Suratul Furqan

O versículo : 33

وَلَا يَأۡتُونَكَ بِمَثَلٍ إِلَّا جِئۡنَٰكَ بِٱلۡحَقِّ وَأَحۡسَنَ تَفۡسِيرًا

Kuma ba za su zo maka da wani misali ba (na qalu-bale) sai Mun zo maka da gaskiya, kuma da mafi kyan bayani



Surata: Suratul Furqan

O versículo : 34

ٱلَّذِينَ يُحۡشَرُونَ عَلَىٰ وُجُوهِهِمۡ إِلَىٰ جَهَنَّمَ أُوْلَـٰٓئِكَ شَرّٞ مَّكَانٗا وَأَضَلُّ سَبِيلٗا

Waxanda za a tashe su zuwa wutar Jahannama a kan fuskokinsu, waxannan su suka fi mummunan matsayi kuma mafiya vatacciyar hanya



Surata: Suratul Furqan

O versículo : 35

وَلَقَدۡ ءَاتَيۡنَا مُوسَى ٱلۡكِتَٰبَ وَجَعَلۡنَا مَعَهُۥٓ أَخَاهُ هَٰرُونَ وَزِيرٗا

Haqiqa kuma Mun bai wa Musa Littafi muka kuma sanya xan’uwansa Haruna tare da shi a matsayin Waziri



Surata: Suratul Furqan

O versículo : 36

فَقُلۡنَا ٱذۡهَبَآ إِلَى ٱلۡقَوۡمِ ٱلَّذِينَ كَذَّبُواْ بِـَٔايَٰتِنَا فَدَمَّرۡنَٰهُمۡ تَدۡمِيرٗا

Sai Muka ce: “Ku tafi zuwa ga mutanen da suka qaryata ayoyinmu, sai Muka hallaka su hallakarwa mai tsanani!”



Surata: Suratul Furqan

O versículo : 37

وَقَوۡمَ نُوحٖ لَّمَّا كَذَّبُواْ ٱلرُّسُلَ أَغۡرَقۡنَٰهُمۡ وَجَعَلۡنَٰهُمۡ لِلنَّاسِ ءَايَةٗۖ وَأَعۡتَدۡنَا لِلظَّـٰلِمِينَ عَذَابًا أَلِيمٗا

Mutanen Nuhu kuma lokacin da suka qaryata manzanni[1] sai Muka nutsar da su, Muka kuma sanya su wa’azi ga mutane, kuma Muka tanadi azaba mai raxaxi ga azzalumai


1- Watau ta hanyar qaryata Annabi Nuhu(), domin saqon duk manzanni guda xaya ne, shi ne kaxaita Allah da bauta.


Surata: Suratul Furqan

O versículo : 38

وَعَادٗا وَثَمُودَاْ وَأَصۡحَٰبَ ٱلرَّسِّ وَقُرُونَۢا بَيۡنَ ذَٰلِكَ كَثِيرٗا

Kuma (Muka hallakar da) Adawa da Samudawa da kuma mutanen (rijiyar) Rassu, da kuma wasu al’ummu masu yawa tsakanin hakan



Surata: Suratul Furqan

O versículo : 39

وَكُلّٗا ضَرَبۡنَا لَهُ ٱلۡأَمۡثَٰلَۖ وَكُلّٗا تَبَّرۡنَا تَتۡبِيرٗا

Kowannensu kuwa Mun ba shi misalai; kuma kowannensu Mun hallaka shi mummunar hallakawa



Surata: Suratul Furqan

O versículo : 40

وَلَقَدۡ أَتَوۡاْ عَلَى ٱلۡقَرۡيَةِ ٱلَّتِيٓ أُمۡطِرَتۡ مَطَرَ ٱلسَّوۡءِۚ أَفَلَمۡ يَكُونُواْ يَرَوۡنَهَاۚ بَلۡ كَانُواْ لَا يَرۡجُونَ نُشُورٗا

Haqiqa kuma (su mutanen Makka) sun bi ta alqaryar nan wadda aka yi wa ruwan azaba. Shin ba su kasance suna ganin ta ba ne? Ba haka ba ne, sun dai kasance ne ba sa tsammanin tashin alqiyama



Surata: Suratul Furqan

O versículo : 41

وَإِذَا رَأَوۡكَ إِن يَتَّخِذُونَكَ إِلَّا هُزُوًا أَهَٰذَا ٱلَّذِي بَعَثَ ٱللَّهُ رَسُولًا

Idan kuma suka gan ka ba sa riqon ka sai abin yi wa izgili, (suna cewa): “Yanzu wannan ne wanda Allah ya aiko Manzo?



Surata: Suratul Furqan

O versículo : 42

إِن كَادَ لَيُضِلُّنَا عَنۡ ءَالِهَتِنَا لَوۡلَآ أَن صَبَرۡنَا عَلَيۡهَاۚ وَسَوۡفَ يَعۡلَمُونَ حِينَ يَرَوۡنَ ٱلۡعَذَابَ مَنۡ أَضَلُّ سَبِيلًا

“Lalle saura qiris ya vatar da mu daga ababen bautarmu, ba don mun yi haquri a kansu ba.” Ba da daxewa ba kuwa za su san wanda ya fi vatan hanya yayin da za su ga azaba



Surata: Suratul Furqan

O versículo : 43

أَرَءَيۡتَ مَنِ ٱتَّخَذَ إِلَٰهَهُۥ هَوَىٰهُ أَفَأَنتَ تَكُونُ عَلَيۡهِ وَكِيلًا

Shin ka ga wanda ya mayar da son zuciyarsa (shi ne) abin bautarsa, to yanzu kai za ka zama mai kiyaye shi (daga bin son zuciyarsa)?



Surata: Suratul Furqan

O versículo : 44

أَمۡ تَحۡسَبُ أَنَّ أَكۡثَرَهُمۡ يَسۡمَعُونَ أَوۡ يَعۡقِلُونَۚ إِنۡ هُمۡ إِلَّا كَٱلۡأَنۡعَٰمِ بَلۡ هُمۡ أَضَلُّ سَبِيلًا

Ko kuwa kana tsammanin cewa yawancinsu suna ji ne (na fahimta) ko suna hankalta? Ai su ba wasu ba ne illa kamar dabbobi; a’a su ne ma suka fi (dabbobi) vace hanya



Surata: Suratul Furqan

O versículo : 45

أَلَمۡ تَرَ إِلَىٰ رَبِّكَ كَيۡفَ مَدَّ ٱلظِّلَّ وَلَوۡ شَآءَ لَجَعَلَهُۥ سَاكِنٗا ثُمَّ جَعَلۡنَا ٱلشَّمۡسَ عَلَيۡهِ دَلِيلٗا

Shin ba ka ganin (irin aikin) Ubangijinka yadda ya shimfixa inuwa, da kuwa ya ga dama da sai ya sanya ta a tsaye cak, sannan Muka sanya rana dalilin samuwarta (inuwar)



Surata: Suratul Furqan

O versículo : 46

ثُمَّ قَبَضۡنَٰهُ إِلَيۡنَا قَبۡضٗا يَسِيرٗا

Sannan Muka riqa janye ta da kaxan-kaxan[1]


1- Watau tana raguwa gwargwadon xagawar rana, har ya zamanto ta gushe gaba xaya.


Surata: Suratul Furqan

O versículo : 47

وَهُوَ ٱلَّذِي جَعَلَ لَكُمُ ٱلَّيۡلَ لِبَاسٗا وَٱلنَّوۡمَ سُبَاتٗا وَجَعَلَ ٱلنَّهَارَ نُشُورٗا

Kuma shi ne wanda ya sanya muku dare ya zama sutura, bacci kuma don hutawa kuma ya sanya rana don watsuwa (wajen neman abinci)



Surata: Suratul Furqan

O versículo : 48

وَهُوَ ٱلَّذِيٓ أَرۡسَلَ ٱلرِّيَٰحَ بُشۡرَۢا بَيۡنَ يَدَيۡ رَحۡمَتِهِۦۚ وَأَنزَلۡنَا مِنَ ٱلسَّمَآءِ مَآءٗ طَهُورٗا

Kuma shi ne wanda ya aiko iska don albishir a gabanin (saukar) rahamarsa. Muka kuma saukar da ruwa mai tsarkakewa daga sama



Surata: Suratul Furqan

O versículo : 49

لِّنُحۡـِۧيَ بِهِۦ بَلۡدَةٗ مَّيۡتٗا وَنُسۡقِيَهُۥ مِمَّا خَلَقۡنَآ أَنۡعَٰمٗا وَأَنَاسِيَّ كَثِيرٗا

Don Mu raya busasshiyar qasa da shi, kuma Mu shayar da dabbobi da mutane masu yawa daga abubuwan da Muka halitta



Surata: Suratul Furqan

O versículo : 50

وَلَقَدۡ صَرَّفۡنَٰهُ بَيۡنَهُمۡ لِيَذَّكَّرُواْ فَأَبَىٰٓ أَكۡثَرُ ٱلنَّاسِ إِلَّا كُفُورٗا

Haqiqa kuma Mun sarrafa shi a tsakaninsu don su wa’azantu[1], sai mafi yawan mutane suka qi (wa’azantuwa) sai kafirci


1- Watau Allah () ya sarrafa hujjoji da dalilai daban-daban a cikin Alqur’ani domin mutane su wa’azantu.