Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 17

سَأُرۡهِقُهُۥ صَعُودًا

Ba da daxewa ba zan xora masa (azaba) mai matsananciyar wahala



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 18

إِنَّهُۥ فَكَّرَ وَقَدَّرَ

Lalle shi ya yi tunani, ya kuma auna (a ransa)



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 19

فَقُتِلَ كَيۡفَ قَدَّرَ

Sai aka la’ane shi, yaya ya yi irin wannan awon?



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 20

ثُمَّ قُتِلَ كَيۡفَ قَدَّرَ

Sannan aka kuma la’antar sa, yaya ya yi wannan awon?



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 21

ثُمَّ نَظَرَ

Sannan ya yi nazari



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 22

ثُمَّ عَبَسَ وَبَسَرَ

Sannan ya xaure fuska, ya kuma murtuke



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 23

ثُمَّ أَدۡبَرَ وَٱسۡتَكۡبَرَ

Sannan ya ba da baya (daga imani) ya kuma yi girman kai



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 24

فَقَالَ إِنۡ هَٰذَآ إِلَّا سِحۡرٞ يُؤۡثَرُ

Sai ya ce: “Wannan (Alqur’ani) ba komai ba ne sai sihiri da aka samo (daga wasu)



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 25

إِنۡ هَٰذَآ إِلَّا قَوۡلُ ٱلۡبَشَرِ

“Wannan ba komai ba ne sai magana irin ta mutane.”



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 26

سَأُصۡلِيهِ سَقَرَ

(Allah ya ce): Da sannu zan shigar da shi (wutar) Saqara



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 27

وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا سَقَرُ

Me ya sanar da kai abin da ake ce wa Saqara?



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 28

لَا تُبۡقِي وَلَا تَذَرُ

Ba ta ragewa kuma ba ta barin (komai)



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 29

لَوَّاحَةٞ لِّلۡبَشَرِ

Mai xaxxaye fata ce



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 30

عَلَيۡهَا تِسۡعَةَ عَشَرَ

Akwai (mala’iku) goma sha tara suna tsaron ta



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 31

وَمَا جَعَلۡنَآ أَصۡحَٰبَ ٱلنَّارِ إِلَّا مَلَـٰٓئِكَةٗۖ وَمَا جَعَلۡنَا عِدَّتَهُمۡ إِلَّا فِتۡنَةٗ لِّلَّذِينَ كَفَرُواْ لِيَسۡتَيۡقِنَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ وَيَزۡدَادَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ إِيمَٰنٗا وَلَا يَرۡتَابَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ وَٱلۡمُؤۡمِنُونَ وَلِيَقُولَ ٱلَّذِينَ فِي قُلُوبِهِم مَّرَضٞ وَٱلۡكَٰفِرُونَ مَاذَآ أَرَادَ ٱللَّهُ بِهَٰذَا مَثَلٗاۚ كَذَٰلِكَ يُضِلُّ ٱللَّهُ مَن يَشَآءُ وَيَهۡدِي مَن يَشَآءُۚ وَمَا يَعۡلَمُ جُنُودَ رَبِّكَ إِلَّا هُوَۚ وَمَا هِيَ إِلَّا ذِكۡرَىٰ لِلۡبَشَرِ

Ba Mu kuwa sanya masu tsaron wutar ba sai mala’iku, ba Mu kuma sanya adadinsu ba sai don fitina ga waxanda suka kafirta, don kuma waxanda aka bai wa littafi su sami yaqini, waxanda kuma suka yi imani su qara imani, waxanda aka bai wa littafi da muminai kuma kada su yi tababa, don kuma waxanda suke da raunin imani a zukatansu da kuma kafirai su ce: “Me Allah Yake nufi da yin misali da wannan (adadin)?” Kamar haka Allah Yake vatar da wanda Ya ga dama, Yake kuma shiryar da wanda Ya ga dama. Ba kuma wanda ya san (yawan) rundunar Ubangijinka sai Shi. Ita (Saqara) kuma ba wata abu ba ce face wa’azi ga mutane



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 32

كَلَّا وَٱلۡقَمَرِ

A’a. Na rantse da wata



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 33

وَٱلَّيۡلِ إِذۡ أَدۡبَرَ

Da kuma dare idan ya ba da baya



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 34

وَٱلصُّبۡحِ إِذَآ أَسۡفَرَ

Da kuma asuba idan ta bayyana (da haskenta)



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 35

إِنَّهَا لَإِحۡدَى ٱلۡكُبَرِ

Lalle ita (Saqara) tana xaya daga manya-manyan (bala’o’i)



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 36

نَذِيرٗا لِّلۡبَشَرِ

Gargaxi ce ga mutane



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 37

لِمَن شَآءَ مِنكُمۡ أَن يَتَقَدَّمَ أَوۡ يَتَأَخَّرَ

Ga wanda ya ga dama daga cikinku, ya ci gaba ko ya ci baya



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 38

كُلُّ نَفۡسِۭ بِمَا كَسَبَتۡ رَهِينَةٌ

Kowane rai jingina ne ga abin da ya tsuwurwurta[1]


1- Watau jingina ne ga ayyukansu, ko dai su hallakar da shi ko su kuvutar da shi, su ‘yanta shi.


Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 39

إِلَّآ أَصۡحَٰبَ ٱلۡيَمِينِ

Sai dai ga ma’abota dama[1]


1- Watau waxanda za su karvi littattafan ayyukansu ta hannayensu na dama.


Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 40

فِي جَنَّـٰتٖ يَتَسَآءَلُونَ

(Su kam suna) cikin gidajen Aljanna suna tambayar juna



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 41

عَنِ ٱلۡمُجۡرِمِينَ

Game da manyan masu laifuka



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 42

مَا سَلَكَكُمۡ فِي سَقَرَ

(Suna cewa): “Me ya shigar da ku cikin Saqara?”



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 43

قَالُواْ لَمۡ نَكُ مِنَ ٱلۡمُصَلِّينَ

Suka ce: “Ba mu zama daga cikin masallata ba



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 44

وَلَمۡ نَكُ نُطۡعِمُ ٱلۡمِسۡكِينَ

“Kuma ba mu kasance muna ciyar da miskini ba



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 45

وَكُنَّا نَخُوضُ مَعَ ٱلۡخَآئِضِينَ

“Mun kuma kasance muna kutsawa (cikin varna)[1] tare da masu kutsawa


1- Watau suna faxar qarerayi game da Annabi () da Alqur’ani.


Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 46

وَكُنَّا نُكَذِّبُ بِيَوۡمِ ٱلدِّينِ

“Kuma mun kasance muna qaryata ranar sakamako