Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 47

حَتَّىٰٓ أَتَىٰنَا ٱلۡيَقِينُ

“Har mutuwa ta zo mana.”



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 48

فَمَا تَنفَعُهُمۡ شَفَٰعَةُ ٱلشَّـٰفِعِينَ

Saboda haka ceton masu ceto ba zai amfane su ba



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 49

فَمَا لَهُمۡ عَنِ ٱلتَّذۡكِرَةِ مُعۡرِضِينَ

To me ya same su ne suke bijire wa wa’azi?



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 50

كَأَنَّهُمۡ حُمُرٞ مُّسۡتَنفِرَةٞ

Kai ka ce su jakunan jeji ne da aka firgitar



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 51

فَرَّتۡ مِن قَسۡوَرَةِۭ

Da suka guje wa zaki



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 52

بَلۡ يُرِيدُ كُلُّ ٱمۡرِيٕٖ مِّنۡهُمۡ أَن يُؤۡتَىٰ صُحُفٗا مُّنَشَّرَةٗ

A’a, kowane mutum daga cikinsu yana so ne a ba shi takardu buxaxxu[1] (kafin su bi Annabi)


1- Watau a ba shi buxaxxen littafi wanda zai ba shi labari cewa Annabi Muhammadu () Manzon Allah ne.


Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 53

كَلَّاۖ بَل لَّا يَخَافُونَ ٱلۡأٓخِرَةَ

Faufau! A’a, su dai ba sa tsoron ranar lahira ne



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 54

كَلَّآ إِنَّهُۥ تَذۡكِرَةٞ

Tabbas, lalle shi (Alqur’ani) wa’azi ne



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 55

فَمَن شَآءَ ذَكَرَهُۥ

To duk wanda ya ga dama sai ya wa’azantu



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 56

وَمَا يَذۡكُرُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُۚ هُوَ أَهۡلُ ٱلتَّقۡوَىٰ وَأَهۡلُ ٱلۡمَغۡفِرَةِ

Ba sa kuma wa’azantuwa sai idan Allah Ya ga dama. Shi ne Ya cancanci taqawa, kuma Shi ne Ya cancanci yin gafara



Surata: Suratul Qiyama

O versículo : 1

لَآ أُقۡسِمُ بِيَوۡمِ ٱلۡقِيَٰمَةِ

Ina rantsuwa da ranar alqiyama



Surata: Suratul Qiyama

O versículo : 2

وَلَآ أُقۡسِمُ بِٱلنَّفۡسِ ٱللَّوَّامَةِ

Ina kuma rantsuwa da rai mai yawan zargin (kansa)[1]


1- Watau a kan gazawarsa wajen ayyukan alheri ko a kan aikata laifuka.


Surata: Suratul Qiyama

O versículo : 3

أَيَحۡسَبُ ٱلۡإِنسَٰنُ أَلَّن نَّجۡمَعَ عِظَامَهُۥ

Yanzu mutum yana tsammanin ba za Mu tattara qasusuwansa ba?



Surata: Suratul Qiyama

O versículo : 4

بَلَىٰ قَٰدِرِينَ عَلَىٰٓ أَن نُّسَوِّيَ بَنَانَهُۥ

E, (Mu) Masu iko ne a kan Mu daidaita gavovin yatsunsa



Surata: Suratul Qiyama

O versículo : 5

بَلۡ يُرِيدُ ٱلۡإِنسَٰنُ لِيَفۡجُرَ أَمَامَهُۥ

Ba haka ba ne, mutum yana nufi ne kawai ya gurvata gabansa (da savon Allah)



Surata: Suratul Qiyama

O versículo : 6

يَسۡـَٔلُ أَيَّانَ يَوۡمُ ٱلۡقِيَٰمَةِ

Yana tambaya yaushe ne ranar alqiyamar?



Surata: Suratul Qiyama

O versículo : 7

فَإِذَا بَرِقَ ٱلۡبَصَرُ

To lokacin da gani ya ruxe



Surata: Suratul Qiyama

O versículo : 8

وَخَسَفَ ٱلۡقَمَرُ

Wata kuma ya yi duhu



Surata: Suratul Qiyama

O versículo : 9

وَجُمِعَ ٱلشَّمۡسُ وَٱلۡقَمَرُ

Aka kuma haxe rana da wata (a mafitarsu)



Surata: Suratul Qiyama

O versículo : 10

يَقُولُ ٱلۡإِنسَٰنُ يَوۡمَئِذٍ أَيۡنَ ٱلۡمَفَرُّ

A wannan rana ne mutum zai ce: “Ina wurin gudu?”



Surata: Suratul Qiyama

O versículo : 11

كَلَّا لَا وَزَرَ

Faufau, babu mafaka



Surata: Suratul Qiyama

O versículo : 12

إِلَىٰ رَبِّكَ يَوۡمَئِذٍ ٱلۡمُسۡتَقَرُّ

Zuwa ga Ubangijinka ne kawai matabbata take a wannan rana



Surata: Suratul Qiyama

O versículo : 13

يُنَبَّؤُاْ ٱلۡإِنسَٰنُ يَوۡمَئِذِۭ بِمَا قَدَّمَ وَأَخَّرَ

Za a bai wa mutum labari a wannan rana na abin da ya gabatar da kuma (abin da) ya jinkirtar (na ayyukansa)



Surata: Suratul Qiyama

O versículo : 14

بَلِ ٱلۡإِنسَٰنُ عَلَىٰ نَفۡسِهِۦ بَصِيرَةٞ

A’a, shi dai mutum mai shaida ne a kan kansa



Surata: Suratul Qiyama

O versículo : 15

وَلَوۡ أَلۡقَىٰ مَعَاذِيرَهُۥ

Ko da kuwa ya kawo uzururrukansa



Surata: Suratul Qiyama

O versículo : 16

لَا تُحَرِّكۡ بِهِۦ لِسَانَكَ لِتَعۡجَلَ بِهِۦٓ

(Allah ya ce da Annabinsa): Kada ka motsa harshenka da shi (Alqur’ani) don gaggauta (karanta) shi



Surata: Suratul Qiyama

O versículo : 17

إِنَّ عَلَيۡنَا جَمۡعَهُۥ وَقُرۡءَانَهُۥ

Lalle tattara shi (a zuciyarka) da karanta shi yana kanmu



Surata: Suratul Qiyama

O versículo : 18

فَإِذَا قَرَأۡنَٰهُ فَٱتَّبِعۡ قُرۡءَانَهُۥ

Saboda haka idan Muka karanta (maka) shi sai ka bi karatunsa



Surata: Suratul Qiyama

O versículo : 19

ثُمَّ إِنَّ عَلَيۡنَا بَيَانَهُۥ

Sannan kuma bayaninsa yana kanmu



Surata: Suratul Qiyama

O versículo : 20

كَلَّا بَلۡ تُحِبُّونَ ٱلۡعَاجِلَةَ

Haba, ku dai kawai kuna son duniya ne