Surata: Suratul Lail

O versículo : 5

فَأَمَّا مَنۡ أَعۡطَىٰ وَٱتَّقَىٰ

To wanda ya ba da (haqqoqin da ke kansa) ya kuma yi taqawa



Surata: Suratul Lail

O versículo : 6

وَصَدَّقَ بِٱلۡحُسۡنَىٰ

Ya kuma gaskata (sakamako) mafi kyau



Surata: Suratul Lail

O versículo : 7

فَسَنُيَسِّرُهُۥ لِلۡيُسۡرَىٰ

To lalle ne za Mu sauqaqa masa (hanyar) Aljanna



Surata: Suratul Lail

O versículo : 8

وَأَمَّا مَنۢ بَخِلَ وَٱسۡتَغۡنَىٰ

Amma kuma wanda ya yi rowa (da haqqin Allah) ya kuma wadatu (da neman lada)



Surata: Suratul Lail

O versículo : 9

وَكَذَّبَ بِٱلۡحُسۡنَىٰ

Kuma ya qaryata (sakamako) mafi kyau



Surata: Suratul Lail

O versículo : 10

فَسَنُيَسِّرُهُۥ لِلۡعُسۡرَىٰ

To lalle ne za Mu hore masa (hanyar) wuta



Surata: Suratul Lail

O versículo : 11

وَمَا يُغۡنِي عَنۡهُ مَالُهُۥٓ إِذَا تَرَدَّىٰٓ

Dukiyarsa kuma ba za ta amfane shi ba idan ya gangara (cikin wuta)



Surata: Suratul Lail

O versículo : 12

إِنَّ عَلَيۡنَا لَلۡهُدَىٰ

Lalle bayyana hanyar shiriya a kanmu yake



Surata: Suratul Lail

O versículo : 13

وَإِنَّ لَنَا لَلۡأٓخِرَةَ وَٱلۡأُولَىٰ

Kuma lalle lahira da duniya namu ne



Surata: Suratul Lail

O versículo : 14

فَأَنذَرۡتُكُمۡ نَارٗا تَلَظَّىٰ

Don haka ina yi muku gargaxin wata wuta mai ruruwa



Surata: Suratul Lail

O versículo : 15

لَا يَصۡلَىٰهَآ إِلَّا ٱلۡأَشۡقَى

Ba mai shigar ta sai mafi tsiyacewa



Surata: Suratul Lail

O versículo : 16

ٱلَّذِي كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰ

Wanda ya qaryata ya kuma ba da baya



Surata: Suratul Lail

O versículo : 17

وَسَيُجَنَّبُهَا ٱلۡأَتۡقَى

Kuma lalle za a nesantar da mafi taqawa[1] daga gare ta


1- Da dama daga cikin malaman tafsiri sun bayyana cewa a nan ana nufin Abubakar As-Siddiq ().


Surata: Suratul Lail

O versículo : 18

ٱلَّذِي يُؤۡتِي مَالَهُۥ يَتَزَكَّىٰ

Wanda yake ba da dukiyarsa yana neman tsarkaka



Surata: Suratul Lail

O versículo : 19

وَمَا لِأَحَدٍ عِندَهُۥ مِن نِّعۡمَةٖ تُجۡزَىٰٓ

Ba kuwa wani da ya yi masa wata ni’ima da za a saka masa (a kanta)[1]


1- Watau ba yana ciyar da dukiyarsa ne don ya saka wa wani a kan wata ni’ima da ya yi masa ba.


Surata: Suratul Lail

O versículo : 20

إِلَّا ٱبۡتِغَآءَ وَجۡهِ رَبِّهِ ٱلۡأَعۡلَىٰ

Sai dai don neman Fuskar Ubangijinsa Maxaukaki



Surata: Suratul Lail

O versículo : 21

وَلَسَوۡفَ يَرۡضَىٰ

Kuma lalle zai yarda (da sakamakon da za a ba shi)[1]


1- Watau gidan Aljanna a lahira.


Surata: Suratud Dhuha

O versículo : 1

وَٱلضُّحَىٰ

Na rantse da lokacin hantsi



Surata: Suratud Dhuha

O versículo : 2

وَٱلَّيۡلِ إِذَا سَجَىٰ

Da kuma dare idan ya yi tsit[1]


1- Watau ya lulluve komai da duhunsa, mutane su shiga mazaunansu don su yi barci.


Surata: Suratud Dhuha

O versículo : 3

مَا وَدَّعَكَ رَبُّكَ وَمَا قَلَىٰ

Ubangijinka bai bar ka ba, kuma bai qi ka ba



Surata: Suratud Dhuha

O versículo : 4

وَلَلۡأٓخِرَةُ خَيۡرٞ لَّكَ مِنَ ٱلۡأُولَىٰ

Kuma lalle lahira ta fi maka alheri a kan duniya



Surata: Suratud Dhuha

O versículo : 5

وَلَسَوۡفَ يُعۡطِيكَ رَبُّكَ فَتَرۡضَىٰٓ

Kuma lalle Ubangijinka zai ba ka har sai ka yarda (da abin da Ya ba ka)



Surata: Suratud Dhuha

O versículo : 6

أَلَمۡ يَجِدۡكَ يَتِيمٗا فَـَٔاوَىٰ

Shin bai same ka maraya ba sai Ya haxa ka (da mai kula da kai)?



Surata: Suratud Dhuha

O versículo : 7

وَوَجَدَكَ ضَآلّٗا فَهَدَىٰ

Ya kuma same ka marashin shiriya Ya shiryar (da kai)?



Surata: Suratud Dhuha

O versículo : 8

وَوَجَدَكَ عَآئِلٗا فَأَغۡنَىٰ

Ya kuma same ka matalauci Ya wadata (ka)?



Surata: Suratud Dhuha

O versículo : 9

فَأَمَّا ٱلۡيَتِيمَ فَلَا تَقۡهَرۡ

Don haka maraya fa kada ka yi masa fin qarfi



Surata: Suratud Dhuha

O versículo : 10

وَأَمَّا ٱلسَّآئِلَ فَلَا تَنۡهَرۡ

Mai tambaya[1] kuma kada ka daka masa tsawa


1- Watau mai neman taimako saboda buqata, ko mai tambaya don neman sani.


Surata: Suratud Dhuha

O versículo : 11

وَأَمَّا بِنِعۡمَةِ رَبِّكَ فَحَدِّثۡ

Amma kuma game da ni’imar Ubangijinka sai ka ba da labari



Surata: Suratus Sharh

O versículo : 1

أَلَمۡ نَشۡرَحۡ لَكَ صَدۡرَكَ

Shin ba Mu yalwata maka qirjinka ba[1]?


1- Watau ya hore masa son sauraren wahayin da yake yiwo masa da kuma juriya a kan gallazawar mutanensa.


Surata: Suratus Sharh

O versículo : 2

وَوَضَعۡنَا عَنكَ وِزۡرَكَ

Muka kuma sauke maka nauye-nauyenka[1]?


1- Watau Allah () ya gafarta masa duk wasu laifuka na baya da na nan gaba idan za su samu.