Surata: Suratus Sharh

O versículo : 3

ٱلَّذِيٓ أَنقَضَ ظَهۡرَكَ

Wanda ya nauyayi bayanka?



Surata: Suratus Sharh

O versículo : 4

وَرَفَعۡنَا لَكَ ذِكۡرَكَ

Muka kuma xaukaka maka ambatonka[1]?


1- Watau kamar ambatonsa a cikin kiran salla da iqama da tahiya da sauransu.


Surata: Suratus Sharh

O versículo : 5

فَإِنَّ مَعَ ٱلۡعُسۡرِ يُسۡرًا

To lalle tsanani yana tare da sauqi



Surata: Suratus Sharh

O versículo : 6

إِنَّ مَعَ ٱلۡعُسۡرِ يُسۡرٗا

Lalle tsananin yana tare da sauqi



Surata: Suratus Sharh

O versículo : 7

فَإِذَا فَرَغۡتَ فَٱنصَبۡ

Saboda haka idan ka gama (harkokinka) sai ka kafu (wajen bautar Allah)



Surata: Suratus Sharh

O versículo : 8

وَإِلَىٰ رَبِّكَ فَٱرۡغَب

Sannan kuma ka yi kwaxayi wajen Ubangijinka kawai



Surata: Suratut Tin

O versículo : 1

وَٱلتِّينِ وَٱلزَّيۡتُونِ

Na rantse da vaure da zaitun[1]


1- Watau wuraren tsirowarsu, watau Sham, ko kuma su kansu waxanan bishiyoyin.


Surata: Suratut Tin

O versículo : 2

وَطُورِ سِينِينَ

Da (dutsen) Xuri Sinina



Surata: Suratut Tin

O versículo : 3

وَهَٰذَا ٱلۡبَلَدِ ٱلۡأَمِينِ

Da wannan garin amintacce (watau Makka)



Surata: Suratut Tin

O versículo : 4

لَقَدۡ خَلَقۡنَا ٱلۡإِنسَٰنَ فِيٓ أَحۡسَنِ تَقۡوِيمٖ

Haqiqa Mun halicci mutum a kan mafi kyan diri



Surata: Suratut Tin

O versículo : 5

ثُمَّ رَدَدۡنَٰهُ أَسۡفَلَ سَٰفِلِينَ

Sannan Muka mayar da shi mafi qasqancin qasqantattu[1]


1- Watau ya mayar da shi tsoho tukuf a duniya, ko kuma a lahira ya zamanto xan wuta.


Surata: Suratut Tin

O versículo : 6

إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ فَلَهُمۡ أَجۡرٌ غَيۡرُ مَمۡنُونٖ

Sai fa waxanda suka yi imani suka kuma yi ayyuka nagari, to su kam suna da lada ba mai yankewa ba



Surata: Suratut Tin

O versículo : 7

فَمَا يُكَذِّبُكَ بَعۡدُ بِٱلدِّينِ

To (kai kafiri) me ya sa kake qaryata ranar sakamako bayan haka?



Surata: Suratut Tin

O versículo : 8

أَلَيۡسَ ٱللَّهُ بِأَحۡكَمِ ٱلۡحَٰكِمِينَ

Ashe Allah ba Shi ne Mafi iya hukuncin masu hukunci ba?



Surata: Suratul Alaq

O versículo : 1

ٱقۡرَأۡ بِٱسۡمِ رَبِّكَ ٱلَّذِي خَلَقَ

Ka yi karatu da sunan Ubangijinka, Wanda Ya yi halitta



Surata: Suratul Alaq

O versículo : 2

خَلَقَ ٱلۡإِنسَٰنَ مِنۡ عَلَقٍ

Ya halicci mutum daga gudan jini[1]


1- Watau bayan yana xigon maniyyi.


Surata: Suratul Alaq

O versículo : 3

ٱقۡرَأۡ وَرَبُّكَ ٱلۡأَكۡرَمُ

Ka yi karatu alhali Ubangijinka Shi ne mafi karamci



Surata: Suratul Alaq

O versículo : 4

ٱلَّذِي عَلَّمَ بِٱلۡقَلَمِ

Wanda Ya koyar ta (hanyar) alqalami



Surata: Suratul Alaq

O versículo : 5

عَلَّمَ ٱلۡإِنسَٰنَ مَا لَمۡ يَعۡلَمۡ

Ya koyar da mutum abin da bai sani ba



Surata: Suratul Alaq

O versículo : 6

كَلَّآ إِنَّ ٱلۡإِنسَٰنَ لَيَطۡغَىٰٓ

Tabbas! Lalle (jinsin) mutum haqiqa yana yin xagawa



Surata: Suratul Alaq

O versículo : 7

أَن رَّءَاهُ ٱسۡتَغۡنَىٰٓ

Don ya ga kansa yana cikin wadata



Surata: Suratul Alaq

O versículo : 8

إِنَّ إِلَىٰ رَبِّكَ ٱلرُّجۡعَىٰٓ

Lalle kuma zuwa ga Ubangijinka ne makomar (taka) take



Surata: Suratul Alaq

O versículo : 9

أَرَءَيۡتَ ٱلَّذِي يَنۡهَىٰ

Ka ba ni labarin wanda yake hana



Surata: Suratul Alaq

O versículo : 10

عَبۡدًا إِذَا صَلَّىٰٓ

Bawa yayin da ya yi salla



Surata: Suratul Alaq

O versículo : 11

أَرَءَيۡتَ إِن كَانَ عَلَى ٱلۡهُدَىٰٓ

Ka ba ni labari idan (shi Bawan) ya kasance a kan shiriya



Surata: Suratul Alaq

O versículo : 12

أَوۡ أَمَرَ بِٱلتَّقۡوَىٰٓ

Ko kuma ya yi umarni da taqawa



Surata: Suratul Alaq

O versículo : 13

أَرَءَيۡتَ إِن كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰٓ

Ka ba ni labari idan (shi mai hanawar) ya qaryata ya kuma ba da baya



Surata: Suratul Alaq

O versículo : 14

أَلَمۡ يَعۡلَم بِأَنَّ ٱللَّهَ يَرَىٰ

Shin bai sani ba cewa lalle Allah Yana ganin (sa)?



Surata: Suratul Alaq

O versículo : 15

كَلَّا لَئِن لَّمۡ يَنتَهِ لَنَسۡفَعَۢا بِٱلنَّاصِيَةِ

A’aha! Tabbas idan bai hanu ba to za Mu ja shi ta makwarkwaxar kai



Surata: Suratul Alaq

O versículo : 16

نَاصِيَةٖ كَٰذِبَةٍ خَاطِئَةٖ

Makwarkwaxar kai mai qaryatawa, mai aikata laifi