Surata: Suratux Xur

O versículo : 31

قُلۡ تَرَبَّصُواْ فَإِنِّي مَعَكُم مِّنَ ٱلۡمُتَرَبِّصِينَ

Ka ce, “To ku saurara, ni ma lalle ina cikin masu sauraron.”



Surata: Suratux Xur

O versículo : 32

أَمۡ تَأۡمُرُهُمۡ أَحۡلَٰمُهُم بِهَٰذَآۚ أَمۡ هُمۡ قَوۡمٞ طَاغُونَ

Ko kuwa hankullansu ne suke umartar su da wannan? A’a, su dai mutane ne masu tsaurin kai



Surata: Suratux Xur

O versículo : 33

أَمۡ يَقُولُونَ تَقَوَّلَهُۥۚ بَل لَّا يُؤۡمِنُونَ

Ko kuwa suna cewa: “Ya qago shi?” A’a, su dai ba sa yin imani ne kawai



Surata: Suratux Xur

O versículo : 34

فَلۡيَأۡتُواْ بِحَدِيثٖ مِّثۡلِهِۦٓ إِن كَانُواْ صَٰدِقِينَ

To su zo da wani zance irinsa idan sun kasance masu gaskiya



Surata: Suratux Xur

O versículo : 35

أَمۡ خُلِقُواْ مِنۡ غَيۡرِ شَيۡءٍ أَمۡ هُمُ ٱلۡخَٰلِقُونَ

Ko kuwa an halicce su ne ba da wani mai halitta ba, ko kuwa su ne masu halittar (kansu)?



Surata: Suratux Xur

O versículo : 36

أَمۡ خَلَقُواْ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَۚ بَل لَّا يُوقِنُونَ

Ko kuwa su suka halicci sammai da qasa? A’a, ba sa dai sakankancewa ne



Surata: Suratux Xur

O versículo : 37

أَمۡ عِندَهُمۡ خَزَآئِنُ رَبِّكَ أَمۡ هُمُ ٱلۡمُصَۜيۡطِرُونَ

Ko kuwa taskokin Ubangijinka suna wurinsu ne, ko kuwa su ne masu iko?



Surata: Suratux Xur

O versículo : 38

أَمۡ لَهُمۡ سُلَّمٞ يَسۡتَمِعُونَ فِيهِۖ فَلۡيَأۡتِ مُسۡتَمِعُهُم بِسُلۡطَٰنٖ مُّبِينٍ

Ko kuwa suna da wani tsani ne da suke jiyo (zancen Allah) ta kansa[1]? To mai jiyowar tasu ya zo da wata hujja mabayyaniya


1- Watau cewa su ne masu gaskiya, Annabi () maqaryaci ne?


Surata: Suratux Xur

O versículo : 39

أَمۡ لَهُ ٱلۡبَنَٰتُ وَلَكُمُ ٱلۡبَنُونَ

Ko kuwa Shi ne zai zama mai ‘ya’ya mata, ku kuwa ku zamanto da ‘ya’ya maza?



Surata: Suratux Xur

O versículo : 40

أَمۡ تَسۡـَٔلُهُمۡ أَجۡرٗا فَهُم مِّن مَّغۡرَمٖ مُّثۡقَلُونَ

Ko kuwa kana tambayar su wani lada ne, saboda haka bashi ya yi musu nauyi?



Surata: Suratux Xur

O versículo : 41

أَمۡ عِندَهُمُ ٱلۡغَيۡبُ فَهُمۡ يَكۡتُبُونَ

Ko kuwa sun san gaibu ne, saboda haka su ne suke rubutawa



Surata: Suratux Xur

O versículo : 42

أَمۡ يُرِيدُونَ كَيۡدٗاۖ فَٱلَّذِينَ كَفَرُواْ هُمُ ٱلۡمَكِيدُونَ

Ko kuwa suna nufin (yi maka) makirci ne? To waxanda suka kafirce su ne waxanda makircinsu zai kama su



Surata: Suratux Xur

O versículo : 43

أَمۡ لَهُمۡ إِلَٰهٌ غَيۡرُ ٱللَّهِۚ سُبۡحَٰنَ ٱللَّهِ عَمَّا يُشۡرِكُونَ

Ko kuwa suna da wani abin bauta ne ba Allah ba? Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke tara (Shi da shi)



Surata: Suratux Xur

O versículo : 44

وَإِن يَرَوۡاْ كِسۡفٗا مِّنَ ٱلسَّمَآءِ سَاقِطٗا يَقُولُواْ سَحَابٞ مَّرۡكُومٞ

Da kuwa za su ga wani yanki na azaba mai faxowa daga sama da sai su ce: “Hadari ne haxaxxe.”



Surata: Suratux Xur

O versículo : 45

فَذَرۡهُمۡ حَتَّىٰ يُلَٰقُواْ يَوۡمَهُمُ ٱلَّذِي فِيهِ يُصۡعَقُونَ

To ka rabu da su har sai sun haxu da ranarsu wadda za a karvi rayukansu a cikinta



Surata: Suratux Xur

O versículo : 46

يَوۡمَ لَا يُغۡنِي عَنۡهُمۡ كَيۡدُهُمۡ شَيۡـٔٗا وَلَا هُمۡ يُنصَرُونَ

Ranar da makircinsu ba zai maganta musu komai ba, kuma su ba za a taimake su ba



Surata: Suratux Xur

O versículo : 47

وَإِنَّ لِلَّذِينَ ظَلَمُواْ عَذَابٗا دُونَ ذَٰلِكَ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَهُمۡ لَا يَعۡلَمُونَ

Lalle kuma waxanda suka yi zalunci suna da wata azabar daban[1] ban da wannan (ta lahira), sai dai kuma mafi yawansu ba su sani ba


1- Watau a nan duniya ta hanyar kisa a wajen yaqi ko kamu a matsayin ribatattu ko kuma azabar qabari bayan sun mutu.


Surata: Suratux Xur

O versículo : 48

وَٱصۡبِرۡ لِحُكۡمِ رَبِّكَ فَإِنَّكَ بِأَعۡيُنِنَاۖ وَسَبِّحۡ بِحَمۡدِ رَبِّكَ حِينَ تَقُومُ

Kuma ka yi haquri da hukuncin Ubangijika, don ko lalle kana qarqashin lurarmu; kuma ka yi tasbihi da yabon Ubangijinka lokacin da za ka tashi (daga bacci)



Surata: Suratux Xur

O versículo : 49

وَمِنَ ٱلَّيۡلِ فَسَبِّحۡهُ وَإِدۡبَٰرَ ٱلنُّجُومِ

Da daddare kuma sai ka tsarkake Shi da kuma lokacin da taurari suka ba da baya



Surata: Suratun Najm

O versículo : 1

وَٱلنَّجۡمِ إِذَا هَوَىٰ

Na rantse da tauraro yayin da ya faxi



Surata: Suratun Najm

O versículo : 2

مَا ضَلَّ صَاحِبُكُمۡ وَمَا غَوَىٰ

Mutumin naku[1] bai vata ba, kuma bai kauce hanya ba


1- Watau Annabi Muhammadu ().


Surata: Suratun Najm

O versículo : 3

وَمَا يَنطِقُ عَنِ ٱلۡهَوَىٰٓ

Kuma ba ya yin magana bisa son rai



Surata: Suratun Najm

O versículo : 4

إِنۡ هُوَ إِلَّا وَحۡيٞ يُوحَىٰ

Shi (Alqur’ani) ba wani abu ne ba in ban da wahayi da ake yiwo (masa)



Surata: Suratun Najm

O versículo : 5

عَلَّمَهُۥ شَدِيدُ ٱلۡقُوَىٰ

Mai tsananin qarfi ne (watau Jibrilu) ya koyar da shi



Surata: Suratun Najm

O versículo : 6

ذُو مِرَّةٖ فَٱسۡتَوَىٰ

Mai kyawawan halitta ne, sai ya daidaita



Surata: Suratun Najm

O versículo : 7

وَهُوَ بِٱلۡأُفُقِ ٱلۡأَعۡلَىٰ

Alhali kuwa shi yana a sassa na can sama



Surata: Suratun Najm

O versículo : 8

ثُمَّ دَنَا فَتَدَلَّىٰ

Sannan sai ya kusanto, sai ya qara matsawa[1]


1- Watau Jibrilu () ya kusanto Annabi () ya matso kusa don yi masa wahayi.


Surata: Suratun Najm

O versículo : 9

فَكَانَ قَابَ قَوۡسَيۡنِ أَوۡ أَدۡنَىٰ

Sai ya kasance kamar kusancin kamu biyu ko qasa da haka



Surata: Suratun Najm

O versículo : 10

فَأَوۡحَىٰٓ إِلَىٰ عَبۡدِهِۦ مَآ أَوۡحَىٰ

Sannan (Allah) Ya yiyo wahayin abin da Ya yi wahayi zuwa ga Bawansa (Ma’aiki)



Surata: Suratun Najm

O versículo : 11

مَا كَذَبَ ٱلۡفُؤَادُ مَا رَأَىٰٓ

Zuciyar (ta Ma’aiki) ba ta yi qaryar abin da ta gani ba