Surata: Suratun Nazi’at

O versículo : 21

فَكَذَّبَ وَعَصَىٰ

Sai ya qaryata ya kuma kangare



Surata: Suratun Nazi’at

O versículo : 22

ثُمَّ أَدۡبَرَ يَسۡعَىٰ

Sannan ya ba da baya yana ta gaggawa



Surata: Suratun Nazi’at

O versículo : 23

فَحَشَرَ فَنَادَىٰ

Sai ya tattara (jama’arsa) sai ya yi shela



Surata: Suratun Nazi’at

O versículo : 24

فَقَالَ أَنَا۠ رَبُّكُمُ ٱلۡأَعۡلَىٰ

Sai ya ce, “Ni ne ubangijinku mafi girma!”



Surata: Suratun Nazi’at

O versículo : 25

فَأَخَذَهُ ٱللَّهُ نَكَالَ ٱلۡأٓخِرَةِ وَٱلۡأُولَىٰٓ

Saboda haka Allah Ya kama shi da azabar lahira (watau Jahannama) da ta duniya (watau nutse wa a ruwa)



Surata: Suratun Nazi’at

O versículo : 26

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَعِبۡرَةٗ لِّمَن يَخۡشَىٰٓ

Lalle a game da wannan tabbas akwai izina ga wanda yake tsoron (Allah)



Surata: Suratun Nazi’at

O versículo : 27

ءَأَنتُمۡ أَشَدُّ خَلۡقًا أَمِ ٱلسَّمَآءُۚ بَنَىٰهَا

Yanzu ku ne halittarku ta fi tsanani ko kuwa sama wadda Shi ne Ya gina ta?



Surata: Suratun Nazi’at

O versículo : 28

رَفَعَ سَمۡكَهَا فَسَوَّىٰهَا

Ya xaukaka rufinta Ya kuma daidaita ta[1]


1- Watau ya zama babu wata varaka ko tsagewa ko wani aibi tare da ita.


Surata: Suratun Nazi’at

O versículo : 29

وَأَغۡطَشَ لَيۡلَهَا وَأَخۡرَجَ ضُحَىٰهَا

Ya lulluve darenta da duhu Ya kuma fitar da hasken hantsinta



Surata: Suratun Nazi’at

O versículo : 30

وَٱلۡأَرۡضَ بَعۡدَ ذَٰلِكَ دَحَىٰهَآ

Qasa kuma bayan haka Ya shimfixa ta



Surata: Suratun Nazi’at

O versículo : 31

أَخۡرَجَ مِنۡهَا مَآءَهَا وَمَرۡعَىٰهَا

Ya fitar da ruwanta da makiyayarta daga gare ta



Surata: Suratun Nazi’at

O versículo : 32

وَٱلۡجِبَالَ أَرۡسَىٰهَا

Duwatsu kuma Ya kafa su



Surata: Suratun Nazi’at

O versículo : 33

مَتَٰعٗا لَّكُمۡ وَلِأَنۡعَٰمِكُمۡ

Don jin daxinku da na dabbobinku



Surata: Suratun Nazi’at

O versículo : 34

فَإِذَا جَآءَتِ ٱلطَّآمَّةُ ٱلۡكُبۡرَىٰ

Sannan idan mafi girman busar qaho ta zo (watau busa ta biyu)



Surata: Suratun Nazi’at

O versículo : 35

يَوۡمَ يَتَذَكَّرُ ٱلۡإِنسَٰنُ مَا سَعَىٰ

A ranar da mutum zai tuna abin da ya aikata



Surata: Suratun Nazi’at

O versículo : 36

وَبُرِّزَتِ ٱلۡجَحِيمُ لِمَن يَرَىٰ

Aka kuma bayyana (wutar) Jahimu ga kowane mai gani



Surata: Suratun Nazi’at

O versículo : 37

فَأَمَّا مَن طَغَىٰ

To (a wannan ranar) duk wanda ya yi xagawa



Surata: Suratun Nazi’at

O versículo : 38

وَءَاثَرَ ٱلۡحَيَوٰةَ ٱلدُّنۡيَا

Ya kuma fifita rayuwar duniya



Surata: Suratun Nazi’at

O versículo : 39

فَإِنَّ ٱلۡجَحِيمَ هِيَ ٱلۡمَأۡوَىٰ

To lalle (wutar) Jahimu ita ce makoma



Surata: Suratun Nazi’at

O versículo : 40

وَأَمَّا مَنۡ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ وَنَهَى ٱلنَّفۡسَ عَنِ ٱلۡهَوَىٰ

Duk wanda kuma ya ji tsoron tsayuwa gaban Ubangijinsa, ya kuma hana zuciya bin abin da take so



Surata: Suratun Nazi’at

O versículo : 41

فَإِنَّ ٱلۡجَنَّةَ هِيَ ٱلۡمَأۡوَىٰ

To lalle Aljanna ita ce makoma



Surata: Suratun Nazi’at

O versículo : 42

يَسۡـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلسَّاعَةِ أَيَّانَ مُرۡسَىٰهَا

Suna tambayar ka game da alqiyama, yaushe ne lokacinta?



Surata: Suratun Nazi’at

O versículo : 43

فِيمَ أَنتَ مِن ذِكۡرَىٰهَآ

Me ya gama ka da ambaton lokacinta?



Surata: Suratun Nazi’at

O versículo : 44

إِلَىٰ رَبِّكَ مُنتَهَىٰهَآ

Zuwa ga Ubangijinka ne iyakacin saninta yake[1]


1- Watau Allah ne kaxai ya san lokacin aukuwarta.


Surata: Suratun Nazi’at

O versículo : 45

إِنَّمَآ أَنتَ مُنذِرُ مَن يَخۡشَىٰهَا

Kai dai kawai mai gargaxin wanda yake tsoron ta ne



Surata: Suratun Nazi’at

O versículo : 46

كَأَنَّهُمۡ يَوۡمَ يَرَوۡنَهَا لَمۡ يَلۡبَثُوٓاْ إِلَّا عَشِيَّةً أَوۡ ضُحَىٰهَا

Kai ka ce su ranar da za su gan ta ba su zauna ba (a duniya) face wani yammaci ko kuma hantsinta



Surata: Suratu Abasa

O versículo : 1

عَبَسَ وَتَوَلَّىٰٓ

Ya xaure fuska[1], ya kuma ba da baya


1- Shi ne Manzon Allah ().


Surata: Suratu Abasa

O versículo : 2

أَن جَآءَهُ ٱلۡأَعۡمَىٰ

Don makaho[1] ya zo masa


1- Shi ne Abdullahi xan Ummu Maktum, ya zo yana yi wa Annabi () tambaya a lokacin shi kuma yana qoqarin janyo hankalin shugabannin Quraishawa zuwa ga Musulunci.


Surata: Suratu Abasa

O versículo : 3

وَمَا يُدۡرِيكَ لَعَلَّهُۥ يَزَّكَّىٰٓ

Me kuma zai sanar da kai cewa wataqila shi ne zai tsarkaka?



Surata: Suratu Abasa

O versículo : 4

أَوۡ يَذَّكَّرُ فَتَنفَعَهُ ٱلذِّكۡرَىٰٓ

Ko ya wa’azantu, sai wa’azin ya amfane shi?