Surata: Suratu Maryam

O versículo : 85

يَوۡمَ نَحۡشُرُ ٱلۡمُتَّقِينَ إِلَى ٱلرَّحۡمَٰنِ وَفۡدٗا

Ranar da za Mu tayar da masu taqawa zuwa ga (Allah) Mai rahama a matsayin manyan baqi



Surata: Suratu Maryam

O versículo : 86

وَنَسُوقُ ٱلۡمُجۡرِمِينَ إِلَىٰ جَهَنَّمَ وِرۡدٗا

Mu kuma kora kafirai zuwa Jahannama cikin tsananin qishirwa



Surata: Suratu Maryam

O versículo : 87

لَّا يَمۡلِكُونَ ٱلشَّفَٰعَةَ إِلَّا مَنِ ٱتَّخَذَ عِندَ ٱلرَّحۡمَٰنِ عَهۡدٗا

Ba wani mai ikon yin ceto sai wanda yake da alqawari a wurin (Allah) Mai rahama[1]


1- Watau ya riqe alqawarin da ya yi na imani da Allah da manzanninsa.


Surata: Suratu Maryam

O versículo : 88

وَقَالُواْ ٱتَّخَذَ ٱلرَّحۡمَٰنُ وَلَدٗا

Suka kuma ce: “(Allah) Mai rahama (wai) yana da xa



Surata: Suratu Maryam

O versículo : 89

لَّقَدۡ جِئۡتُمۡ شَيۡـًٔا إِدّٗا

Haqiqa kun zo da babban abu (marar daxin ji)



Surata: Suratu Maryam

O versículo : 90

تَكَادُ ٱلسَّمَٰوَٰتُ يَتَفَطَّرۡنَ مِنۡهُ وَتَنشَقُّ ٱلۡأَرۡضُ وَتَخِرُّ ٱلۡجِبَالُ هَدًّا

Sama ta kusa ta kece saboda shi (mummunan furucin), qasa kuma ta tsage, duwatsu kuma su zube su yi rugu-rugu



Surata: Suratu Maryam

O versículo : 91

أَن دَعَوۡاْ لِلرَّحۡمَٰنِ وَلَدٗا

Saboda sun yi da’awar Allah Yana da xa!



Surata: Suratu Maryam

O versículo : 92

وَمَا يَنۢبَغِي لِلرَّحۡمَٰنِ أَن يَتَّخِذَ وَلَدًا

Bai kuwa dace da (Allah) Mai rahama Ya zama Yana da xa ba



Surata: Suratu Maryam

O versículo : 93

إِن كُلُّ مَن فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ إِلَّآ ءَاتِي ٱلرَّحۡمَٰنِ عَبۡدٗا

Ba wani abu da yake cikin sammai da qasa face ya zo wa (Allah) Mai rahama a matsayin bawa



Surata: Suratu Maryam

O versículo : 94

لَّقَدۡ أَحۡصَىٰهُمۡ وَعَدَّهُمۡ عَدّٗا

Lalle Ya kiyaye da su Ya kuma qididdige su sosai



Surata: Suratu Maryam

O versículo : 95

وَكُلُّهُمۡ ءَاتِيهِ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِ فَرۡدًا

Kuma dukkansu kowa zai zo masa a ranar alqiyama shi kaxai



Surata: Suratu Maryam

O versículo : 96

إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ سَيَجۡعَلُ لَهُمُ ٱلرَّحۡمَٰنُ وُدّٗا

Lalle waxanda suka yi imani suka kuma yi aiki na gari, to (Allah) Mai rahama zai sanya musu qauna[1]


1- Watau zanya farin jininsu a zukatan masoyansa a sama da qasa. Shi ma kuma zai qaunace su.


Surata: Suratu Maryam

O versículo : 97

فَإِنَّمَا يَسَّرۡنَٰهُ بِلِسَانِكَ لِتُبَشِّرَ بِهِ ٱلۡمُتَّقِينَ وَتُنذِرَ بِهِۦ قَوۡمٗا لُّدّٗا

To Mun dai sauqaqe shi (Alqur’ani) da harshenka ne don kawai ka yi wa masu taqawa albishir da shi, ka kuma gargaxi mutane masu tsananin jayayya da shi



Surata: Suratu Maryam

O versículo : 98

وَكَمۡ أَهۡلَكۡنَا قَبۡلَهُم مِّن قَرۡنٍ هَلۡ تُحِسُّ مِنۡهُم مِّنۡ أَحَدٍ أَوۡ تَسۡمَعُ لَهُمۡ رِكۡزَۢا

Al’umma nawa Muka hallaka a gabaninsu, shin kana jin xuriyar wani daga cikinsu, ko kuwa kana jin ‘yar muryarsu?



Surata: Suratu Xa Ha

O versículo : 1

طه

Xa Ha[1]


1- Duba Suratul Baqara, aya ta 1, hashiya ta 8.


Surata: Suratu Xa Ha

O versículo : 2

مَآ أَنزَلۡنَا عَلَيۡكَ ٱلۡقُرۡءَانَ لِتَشۡقَىٰٓ

Ba Mu saukar maka da Alqur’ani don ka wahala ba



Surata: Suratu Xa Ha

O versículo : 3

إِلَّا تَذۡكِرَةٗ لِّمَن يَخۡشَىٰ

Sai don wa’azi ga wanda zai ji tsoron (haxuwa da Allah)



Surata: Suratu Xa Ha

O versículo : 4

تَنزِيلٗا مِّمَّنۡ خَلَقَ ٱلۡأَرۡضَ وَٱلسَّمَٰوَٰتِ ٱلۡعُلَى

Saukakke ne daga wanda Ya halicci qasa da sammai masu xaukaka



Surata: Suratu Xa Ha

O versículo : 5

ٱلرَّحۡمَٰنُ عَلَى ٱلۡعَرۡشِ ٱسۡتَوَىٰ

(Allah) Mai rahama, Ya daidaita a kan Al’arshi[1]


1- Duba Suratul A’arafi, aya ta 54, hashiya ta 126.


Surata: Suratu Xa Ha

O versículo : 6

لَهُۥ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَا فِي ٱلۡأَرۡضِ وَمَا بَيۡنَهُمَا وَمَا تَحۡتَ ٱلثَّرَىٰ

Abin da yake sammai da qasa, da abin da yake tsakaninsu da kuma abin da yake qarqashin qasa, (duka) nasa ne



Surata: Suratu Xa Ha

O versículo : 7

وَإِن تَجۡهَرۡ بِٱلۡقَوۡلِ فَإِنَّهُۥ يَعۡلَمُ ٱلسِّرَّ وَأَخۡفَى

Idan kuma ka xaga murya da furuci to lalle Shi Yana sane da sirri da abin da ya fi (sirri) vuya



Surata: Suratu Xa Ha

O versículo : 8

ٱللَّهُ لَآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَۖ لَهُ ٱلۡأَسۡمَآءُ ٱلۡحُسۡنَىٰ

Allah (Shi ne wanda) babu wani abin bauta da gaskiya sai Shi; Yana da sunaye mafiya kyau



Surata: Suratu Xa Ha

O versículo : 9

وَهَلۡ أَتَىٰكَ حَدِيثُ مُوسَىٰٓ

Shin kuwa labarin Musa ya zo maka?



Surata: Suratu Xa Ha

O versículo : 10

إِذۡ رَءَا نَارٗا فَقَالَ لِأَهۡلِهِ ٱمۡكُثُوٓاْ إِنِّيٓ ءَانَسۡتُ نَارٗا لَّعَلِّيٓ ءَاتِيكُم مِّنۡهَا بِقَبَسٍ أَوۡ أَجِدُ عَلَى ٱلنَّارِ هُدٗى

Lokacin da ya gano wuta sai ya ce da iyalinsa: “Ku zauna (a nan), lalle ni fa na hangi wuta, (zan je) ko na zo muku da garwashinta ko kuma in sami mai nuna mini (hanya) a wurin wutar.”



Surata: Suratu Xa Ha

O versículo : 11

فَلَمَّآ أَتَىٰهَا نُودِيَ يَٰمُوسَىٰٓ

To lokacin da ya zo wurinta (wato wutar), sai aka kira shi (cewa): “Ya Musa



Surata: Suratu Xa Ha

O versículo : 12

إِنِّيٓ أَنَا۠ رَبُّكَ فَٱخۡلَعۡ نَعۡلَيۡكَ إِنَّكَ بِٱلۡوَادِ ٱلۡمُقَدَّسِ طُوٗى

“Lalle Ni, Ni ne fa Ubangijinka, sai ka tuve takalmanka; lalle kana a tsarkakakken kwarin Xuwa ne



Surata: Suratu Xa Ha

O versículo : 13

وَأَنَا ٱخۡتَرۡتُكَ فَٱسۡتَمِعۡ لِمَا يُوحَىٰٓ

“Kuma Ni Na zave ka (da manzanci), sai ka ji abin da za a yiwo ma wahayi (da shi)



Surata: Suratu Xa Ha

O versículo : 14

إِنَّنِيٓ أَنَا ٱللَّهُ لَآ إِلَٰهَ إِلَّآ أَنَا۠ فَٱعۡبُدۡنِي وَأَقِمِ ٱلصَّلَوٰةَ لِذِكۡرِيٓ

“Lalle Ni, Ni ne Allah, babu wani abin bauta sai Ni, to ka bauta mini, kuma ka tsai da salla don tuna Ni



Surata: Suratu Xa Ha

O versículo : 15

إِنَّ ٱلسَّاعَةَ ءَاتِيَةٌ أَكَادُ أُخۡفِيهَا لِتُجۡزَىٰ كُلُّ نَفۡسِۭ بِمَا تَسۡعَىٰ

“Lalle alqiyama za ta zo, ina nufin voye ta ne don a saka wa kowanne rai da irin abin da yake aikatawa



Surata: Suratu Xa Ha

O versículo : 16

فَلَا يَصُدَّنَّكَ عَنۡهَا مَن لَّا يُؤۡمِنُ بِهَا وَٱتَّبَعَ هَوَىٰهُ فَتَرۡدَىٰ

“To kada wanda bai yi imani da ita ba ya kuma bi son ransa ya hana ka gaskata ta, sai ka hallaka