Surata: Suratul Haqqa

O versículo : 39

وَمَا لَا تُبۡصِرُونَ

Da kuma abin da ba kwa gani



Surata: Suratul Haqqa

O versículo : 40

إِنَّهُۥ لَقَوۡلُ رَسُولٖ كَرِيمٖ

Lalle shi (Alqur’ani) tabbas zance ne na wani manzo mai girma



Surata: Suratul Haqqa

O versículo : 41

وَمَا هُوَ بِقَوۡلِ شَاعِرٖۚ قَلِيلٗا مَّا تُؤۡمِنُونَ

Shi kuwa ba zancen mawaqi ba ne. Kaxan ne qwarai kuke yin imani



Surata: Suratul Haqqa

O versículo : 42

وَلَا بِقَوۡلِ كَاهِنٖۚ قَلِيلٗا مَّا تَذَكَّرُونَ

Ba kuma zance ne na boka ba. Kaxan ne qwarai kuke wa’azantuwa



Surata: Suratul Haqqa

O versículo : 43

تَنزِيلٞ مِّن رَّبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Shi saukakke ne daga Ubangijin halittu



Surata: Suratul Haqqa

O versículo : 44

وَلَوۡ تَقَوَّلَ عَلَيۡنَا بَعۡضَ ٱلۡأَقَاوِيلِ

Kuma da ya qaga Mana wasu maganganu



Surata: Suratul Haqqa

O versículo : 45

لَأَخَذۡنَا مِنۡهُ بِٱلۡيَمِينِ

Tabbas da Mun kama shi da qarfi



Surata: Suratul Haqqa

O versículo : 46

ثُمَّ لَقَطَعۡنَا مِنۡهُ ٱلۡوَتِينَ

Sannan da Mun yanke masa jijiyar zuciyarsa



Surata: Suratul Haqqa

O versículo : 47

فَمَا مِنكُم مِّنۡ أَحَدٍ عَنۡهُ حَٰجِزِينَ

Sannan kuma ba wani xaya daga cikinku da zai kare shi



Surata: Suratul Haqqa

O versículo : 48

وَإِنَّهُۥ لَتَذۡكِرَةٞ لِّلۡمُتَّقِينَ

Lalle shi (Alqur’ani) wa’azi ne ga masu kiyaye dokokin Allah



Surata: Suratul Haqqa

O versículo : 49

وَإِنَّا لَنَعۡلَمُ أَنَّ مِنكُم مُّكَذِّبِينَ

Lalle kuma Mu Muna sane da cewa a cikinku akwai masu qaryatawa



Surata: Suratul Haqqa

O versículo : 50

وَإِنَّهُۥ لَحَسۡرَةٌ عَلَى ٱلۡكَٰفِرِينَ

Kuma lalle shi tabbas nadama ce ga kafirai



Surata: Suratul Haqqa

O versículo : 51

وَإِنَّهُۥ لَحَقُّ ٱلۡيَقِينِ

Kuma lalle shi tabbas gaskiya ce ta sakankancewa



Surata: Suratul Haqqa

O versículo : 52

فَسَبِّحۡ بِٱسۡمِ رَبِّكَ ٱلۡعَظِيمِ

Saboda haka ka yi tasbihi da sunan Ubangijinka Mai girma



Surata: Suratul Ma’arij

O versículo : 1

سَأَلَ سَآئِلُۢ بِعَذَابٖ وَاقِعٖ

Mai tambaya ya yi tambaya game da wata azaba mai aukuwa[1]


1- Watau wadda Annabi () yake musu kashedi da ita idan sun qi imani. Duba Suratul Anfal, aya ta 32. Mai tambayar kuwa shi ne Nadhru xan Haris.


Surata: Suratul Ma’arij

O versículo : 2

لِّلۡكَٰفِرِينَ لَيۡسَ لَهُۥ دَافِعٞ

Ga kafirai (wadda) ba ta da wani mai kaxe ta



Surata: Suratul Ma’arij

O versículo : 3

مِّنَ ٱللَّهِ ذِي ٱلۡمَعَارِجِ

Daga Allah Mai matattakalai



Surata: Suratul Ma’arij

O versículo : 4

تَعۡرُجُ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ وَٱلرُّوحُ إِلَيۡهِ فِي يَوۡمٖ كَانَ مِقۡدَارُهُۥ خَمۡسِينَ أَلۡفَ سَنَةٖ

Mala’iku tare da Jibrilu suna hawa zuwa gare Shi a cikin wata rana (wadda) gwargwadonta yake daidai da shekara dubu hamsin



Surata: Suratul Ma’arij

O versículo : 5

فَٱصۡبِرۡ صَبۡرٗا جَمِيلًا

Sai ka yi haquri kyakkyawan haquri



Surata: Suratul Ma’arij

O versículo : 6

إِنَّهُمۡ يَرَوۡنَهُۥ بَعِيدٗا

Lalle su suna ganin ta mai nisa ce



Surata: Suratul Ma’arij

O versículo : 7

وَنَرَىٰهُ قَرِيبٗا

Mu kuma Muna ganin ta kusa-kusa



Surata: Suratul Ma’arij

O versículo : 8

يَوۡمَ تَكُونُ ٱلسَّمَآءُ كَٱلۡمُهۡلِ

A ranar da sama za ta kasance kamar narkakkiyar dalma



Surata: Suratul Ma’arij

O versículo : 9

وَتَكُونُ ٱلۡجِبَالُ كَٱلۡعِهۡنِ

Duwatsu kuma su zama kamar kaxaxxiyar auduga (ta gashin tumaki)



Surata: Suratul Ma’arij

O versículo : 10

وَلَا يَسۡـَٔلُ حَمِيمٌ حَمِيمٗا

Kuma aboki ba ya tambayar aboki



Surata: Suratul Ma’arij

O versículo : 11

يُبَصَّرُونَهُمۡۚ يَوَدُّ ٱلۡمُجۡرِمُ لَوۡ يَفۡتَدِي مِنۡ عَذَابِ يَوۡمِئِذِۭ بِبَنِيهِ

(Alhali kuma) ana nuna musu junansu. Mai laifi ya riqa burin ina ma zai fanshi kansa daga azabar wannan rana da ‘ya’yansa



Surata: Suratul Ma’arij

O versículo : 12

وَصَٰحِبَتِهِۦ وَأَخِيهِ

Da matarsa da xan’uwansa



Surata: Suratul Ma’arij

O versículo : 13

وَفَصِيلَتِهِ ٱلَّتِي تُـٔۡوِيهِ

Da danginsa waxanda suke kare shi



Surata: Suratul Ma’arij

O versículo : 14

وَمَن فِي ٱلۡأَرۡضِ جَمِيعٗا ثُمَّ يُنجِيهِ

Da ma duk wanda yake a bayan qasa baki xaya, sannan (fansar) ta tserar da shi



Surata: Suratul Ma’arij

O versículo : 15

كَلَّآۖ إِنَّهَا لَظَىٰ

Faufau! Lalle ita (wutar) Laza ce



Surata: Suratul Ma’arij

O versículo : 16

نَزَّاعَةٗ لِّلشَّوَىٰ

Mai xaxxaye fatar kai