Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 87

أُوْلَـٰٓئِكَ جَزَآؤُهُمۡ أَنَّ عَلَيۡهِمۡ لَعۡنَةَ ٱللَّهِ وَٱلۡمَلَـٰٓئِكَةِ وَٱلنَّاسِ أَجۡمَعِينَ

Waxannan sakamakonsu (shi ne), lalle la’antar Allah za ta tabbata a kansu da ta mala’iku da mutane gaba xaya



Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 88

خَٰلِدِينَ فِيهَا لَا يُخَفَّفُ عَنۡهُمُ ٱلۡعَذَابُ وَلَا هُمۡ يُنظَرُونَ

Suna masu dawwama a cikinta, ba za a sassauta musu azaba ba, kuma ba za a jinkirta musu ba



Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 89

إِلَّا ٱلَّذِينَ تَابُواْ مِنۢ بَعۡدِ ذَٰلِكَ وَأَصۡلَحُواْ فَإِنَّ ٱللَّهَ غَفُورٞ رَّحِيمٌ

Sai fa waxanda suka sake tuba bayan haka, kuma suka gyara (ayyukansu), to lalle Allah Mai gafara ne, Mai jin qai



Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 90

إِنَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ بَعۡدَ إِيمَٰنِهِمۡ ثُمَّ ٱزۡدَادُواْ كُفۡرٗا لَّن تُقۡبَلَ تَوۡبَتُهُمۡ وَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلضَّآلُّونَ

Lalle waxanda suka kafirta bayan imaninsu, sannan suka qara zurfi cikin kafirci, to ba za a karvi tubansu ba, kuma waxannan su ne vatattu



Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 91

إِنَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ وَمَاتُواْ وَهُمۡ كُفَّارٞ فَلَن يُقۡبَلَ مِنۡ أَحَدِهِم مِّلۡءُ ٱلۡأَرۡضِ ذَهَبٗا وَلَوِ ٱفۡتَدَىٰ بِهِۦٓۗ أُوْلَـٰٓئِكَ لَهُمۡ عَذَابٌ أَلِيمٞ وَمَا لَهُم مِّن نَّـٰصِرِينَ

Lalle waxanda suka kafirta, kuma suka mutu alhali suna kafirai, to ba za a tava karvar cikin qasa na zinare daga xayansu ba, ko da zai fanshi kansa da shi. Waxannan suna da wata azaba mai raxaxi kuma ba su da wasu mataimaka



Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 92

لَن تَنَالُواْ ٱلۡبِرَّ حَتَّىٰ تُنفِقُواْ مِمَّا تُحِبُّونَۚ وَمَا تُنفِقُواْ مِن شَيۡءٖ فَإِنَّ ٱللَّهَ بِهِۦ عَلِيمٞ

Ba za ku tava dacewa da aiki na alheri ba har sai kun ciyar daga abin da kuke so, kuma abin da duk kuka ciyar kowane iri ne, to lalle Allah Yana sane da shi