Surata: Suratul Muzzammil

O versículo : 7

إِنَّ لَكَ فِي ٱلنَّهَارِ سَبۡحٗا طَوِيلٗا

Lalle da rana kana da harkoki masu yawa



Surata: Suratul Muzzammil

O versículo : 8

وَٱذۡكُرِ ٱسۡمَ رَبِّكَ وَتَبَتَّلۡ إِلَيۡهِ تَبۡتِيلٗا

Ka kuma ambaci sunan Ubangijinka kuma ka yanke alaqarka da komai don bautarsa



Surata: Suratul Muzzammil

O versículo : 9

رَّبُّ ٱلۡمَشۡرِقِ وَٱلۡمَغۡرِبِ لَآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَ فَٱتَّخِذۡهُ وَكِيلٗا

(Shi ne) Ubangijin mahudar rana da mafaxar rana, babu wani abin bauta wa da gaskiya sai Shi, saboda haka ka riqe Shi Abin dogara



Surata: Suratul Muzzammil

O versículo : 10

وَٱصۡبِرۡ عَلَىٰ مَا يَقُولُونَ وَٱهۡجُرۡهُمۡ هَجۡرٗا جَمِيلٗا

Kuma ka yi haquri a kan abin da suke faxa, kuma ka qaurace musu kyakkyawar qauracewa[1]


1- Watau qauracewar da babu cutarwa a cikinta.


Surata: Suratul Muzzammil

O versículo : 11

وَذَرۡنِي وَٱلۡمُكَذِّبِينَ أُوْلِي ٱلنَّعۡمَةِ وَمَهِّلۡهُمۡ قَلِيلًا

Ka kuma bar ni da masu qaryatawa ma’abota ni’ima, ka kuma xan saurara musu



Surata: Suratul Muzzammil

O versículo : 12

إِنَّ لَدَيۡنَآ أَنكَالٗا وَجَحِيمٗا

Lalle a wurinmu akwai maruruwa da kuma (wutar) Jahimu



Surata: Suratul Muzzammil

O versículo : 13

وَطَعَامٗا ذَا غُصَّةٖ وَعَذَابًا أَلِيمٗا

Da kuma abinci mai shaqewa da kuma azaba mai raxaxi



Surata: Suratul Muzzammil

O versículo : 14

يَوۡمَ تَرۡجُفُ ٱلۡأَرۡضُ وَٱلۡجِبَالُ وَكَانَتِ ٱلۡجِبَالُ كَثِيبٗا مَّهِيلًا

A ranar da qasa da duwatsu za su girgiza, duwatsun kuma su kasance rairayi tilis



Surata: Suratul Muzzammil

O versículo : 15

إِنَّآ أَرۡسَلۡنَآ إِلَيۡكُمۡ رَسُولٗا شَٰهِدًا عَلَيۡكُمۡ كَمَآ أَرۡسَلۡنَآ إِلَىٰ فِرۡعَوۡنَ رَسُولٗا

Lalle Mu Muka aiko muku da Manzo yana mai shaida a kanku kamar yadda Muka aiko wani manzo zuwa ga Fir’auna



Surata: Suratul Muzzammil

O versículo : 16

فَعَصَىٰ فِرۡعَوۡنُ ٱلرَّسُولَ فَأَخَذۡنَٰهُ أَخۡذٗا وَبِيلٗا

Sai Fir’auna ya sava wa Manzon, sai Muka kama shi kamu mai tsanani



Surata: Suratul Muzzammil

O versículo : 17

فَكَيۡفَ تَتَّقُونَ إِن كَفَرۡتُمۡ يَوۡمٗا يَجۡعَلُ ٱلۡوِلۡدَٰنَ شِيبًا

Ta yaya idan kuka kafirta za ku iya kare kanku daga ranar da za ta mayar da yara qanana su zama masu furfura?



Surata: Suratul Muzzammil

O versículo : 18

ٱلسَّمَآءُ مُنفَطِرُۢ بِهِۦۚ كَانَ وَعۡدُهُۥ مَفۡعُولًا

Sama za ta kece saboda ita (ranar). Alqawarinsa ya kasance abin aikatawa ne



Surata: Suratul Muzzammil

O versículo : 19

إِنَّ هَٰذِهِۦ تَذۡكِرَةٞۖ فَمَن شَآءَ ٱتَّخَذَ إِلَىٰ رَبِّهِۦ سَبِيلًا

Lalle wannan wa’azi ne, saboda haka duk wanda ya ga dama sai ya kama hanya zuwa ga Ubangijinsa



Surata: Suratul Muzzammil

O versículo : 20

۞إِنَّ رَبَّكَ يَعۡلَمُ أَنَّكَ تَقُومُ أَدۡنَىٰ مِن ثُلُثَيِ ٱلَّيۡلِ وَنِصۡفَهُۥ وَثُلُثَهُۥ وَطَآئِفَةٞ مِّنَ ٱلَّذِينَ مَعَكَۚ وَٱللَّهُ يُقَدِّرُ ٱلَّيۡلَ وَٱلنَّهَارَۚ عَلِمَ أَن لَّن تُحۡصُوهُ فَتَابَ عَلَيۡكُمۡۖ فَٱقۡرَءُواْ مَا تَيَسَّرَ مِنَ ٱلۡقُرۡءَانِۚ عَلِمَ أَن سَيَكُونُ مِنكُم مَّرۡضَىٰ وَءَاخَرُونَ يَضۡرِبُونَ فِي ٱلۡأَرۡضِ يَبۡتَغُونَ مِن فَضۡلِ ٱللَّهِ وَءَاخَرُونَ يُقَٰتِلُونَ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِۖ فَٱقۡرَءُواْ مَا تَيَسَّرَ مِنۡهُۚ وَأَقِيمُواْ ٱلصَّلَوٰةَ وَءَاتُواْ ٱلزَّكَوٰةَ وَأَقۡرِضُواْ ٱللَّهَ قَرۡضًا حَسَنٗاۚ وَمَا تُقَدِّمُواْ لِأَنفُسِكُم مِّنۡ خَيۡرٖ تَجِدُوهُ عِندَ ٱللَّهِ هُوَ خَيۡرٗا وَأَعۡظَمَ أَجۡرٗاۚ وَٱسۡتَغۡفِرُواْ ٱللَّهَۖ إِنَّ ٱللَّهَ غَفُورٞ رَّحِيمُۢ

Lalle Ubangijinka Yana sane da cewa kai kana tsayawa qasa da kashi biyu cikin uku na dare, da kuma rabinsa, da kuma xaya bisa ukunsa, kai da wata jama’ar da take tare da kai. Allah ne kuma Yake qaddara dare da rana. Ya san kuma cewa, ba za ku iya qididdige (sa’o’insa) ba, don haka sai Ya yafe muku; to sai ku karanta abin da ya sauqaqa daga Alqur’ani. Ya san cewa daga cikinku akwai waxanda za su kasance marasa lafiya, waxansu kuma suna tafiya a bayan qasa don fatauci suna neman falala daga Allah, waxansu kuma suna yin yaqi saboda Allah; to sai ku karanta abin da ya sauqaqa daga gare shi (Alqur’ani). Ku kuma tsayar da salla, ku kuma ba da zakka, kuma ku bai wa Allah rance kyakkyawa[1]. Kuma abin da kuka gabatar wa kanku na wani alheri, to za ku same shi wurin Allah, shi ya fi alheri ya kuma fi girman lada. Ku kuma nemi gafarar Allah; lalle Allah Mai gafara ne, Mai jin qai


1- Watau su ciyar da dukiyoyinsu don Allah wuraren da suka dace.


Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 1

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلۡمُدَّثِّرُ

Ya kai mai lulluva[1]


1- Shi ne Annabi () wanda ya lulluva da tufafinsa don tsoron mala’ikan da ya yi idon huxu da shi a karon farko a kogon Hira.


Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 2

قُمۡ فَأَنذِرۡ

Tashi ka yi gargaxi



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 3

وَرَبَّكَ فَكَبِّرۡ

Kuma ka girmama Ubangijinka



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 4

وَثِيَابَكَ فَطَهِّرۡ

Ka kuma tsarkake tufafinka



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 5

وَٱلرُّجۡزَ فَٱهۡجُرۡ

Ka kuma qaurace wa (bautar) gumaka



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 6

وَلَا تَمۡنُن تَسۡتَكۡثِرُ

Kada kuma ka goranta wa (Ubangijinka) da ganin yawan (ayyukanka na qwarai)[1]


1- Watau kada yawansu ya ruxe shi har ya yi rauni wajen tsayuwa da ayyukan da’awa.


Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 7

وَلِرَبِّكَ فَٱصۡبِرۡ

Ka kuma yi haquri game da Ubangijinka



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 8

فَإِذَا نُقِرَ فِي ٱلنَّاقُورِ

To idan an busa qaho



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 9

فَذَٰلِكَ يَوۡمَئِذٖ يَوۡمٌ عَسِيرٌ

To wannan ranar rana ce mai tsanani



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 10

عَلَى ٱلۡكَٰفِرِينَ غَيۡرُ يَسِيرٖ

A kan kafirai, ba mai sauqi ba ce



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 11

ذَرۡنِي وَمَنۡ خَلَقۡتُ وَحِيدٗا

Ka bar Ni da wanda Na halitta shi kaxai[1]


1- Watau a cikin mahaifiyarsa ba tare da dukiya ko ‘ya’ya ba. Shi ne Al-Walidu xan Mugira wanda ya addabi Annabi ().


Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 12

وَجَعَلۡتُ لَهُۥ مَالٗا مَّمۡدُودٗا

Na kuma yi masa baiwa da dukiya maxuxuwa



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 13

وَبَنِينَ شُهُودٗا

Da kuma ‘ya’ya masu halartar (tarurruka tare da shi)



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 14

وَمَهَّدتُّ لَهُۥ تَمۡهِيدٗا

Na kuma shimfixa masa (kyakkyawar rayuwa) iyakar shinfixawa



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 15

ثُمَّ يَطۡمَعُ أَنۡ أَزِيدَ

Sannan yake kwaxayin in qara (masa)



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 16

كَلَّآۖ إِنَّهُۥ كَانَ لِأٓيَٰتِنَا عَنِيدٗا

Faufau! Lalle shi ya kasance mai tsaurin kai ne ga ayoyinmu