Sura: Suratu Qaf 

Aya : 30

يَوۡمَ نَقُولُ لِجَهَنَّمَ هَلِ ٱمۡتَلَأۡتِ وَتَقُولُ هَلۡ مِن مَّزِيدٖ

A ranar da za Mu ce da Jahannama: “Shin kin cika?” (Ita) kuma ta ce: “Shin akwai wani qari?”



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 42

فِي سَمُومٖ وَحَمِيمٖ

Suna cikin iska mai tsananin zafi da kuma tafasasshen ruwa



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 43

وَظِلّٖ مِّن يَحۡمُومٖ

Da kuma inuwa ta turnuqun hayaqi



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 44

لَّا بَارِدٖ وَلَا كَرِيمٍ

Ba mai sanyi ba, kuma ba mai daraja ba



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 51

ثُمَّ إِنَّكُمۡ أَيُّهَا ٱلضَّآلُّونَ ٱلۡمُكَذِّبُونَ

“Sannan lalle ku kuma waxannan vatattu masu qaryatawa



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 52

لَأٓكِلُونَ مِن شَجَرٖ مِّن زَقُّومٖ

“Tabbas za ku ci daga bishiyar Zaqqumu[1]


1- Watau wata bishiya ce mafi muni da sharri a wutar jahannama.


Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 53

فَمَالِـُٔونَ مِنۡهَا ٱلۡبُطُونَ

“Sannan za ku cika cikunanku da ita



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 54

فَشَٰرِبُونَ عَلَيۡهِ مِنَ ٱلۡحَمِيمِ

“Sannan za ku sha tafasasshen ruwa a kanta



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 55

فَشَٰرِبُونَ شُرۡبَ ٱلۡهِيمِ

“Sannan za ku sha irin shan raquma masu jin qishirwa.”



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 56

هَٰذَا نُزُلُهُمۡ يَوۡمَ ٱلدِّينِ

Wannan ita ce gararsu a ranar sakamako



Sura: Suratut Tahrim

Aya : 6

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ قُوٓاْ أَنفُسَكُمۡ وَأَهۡلِيكُمۡ نَارٗا وَقُودُهَا ٱلنَّاسُ وَٱلۡحِجَارَةُ عَلَيۡهَا مَلَـٰٓئِكَةٌ غِلَاظٞ شِدَادٞ لَّا يَعۡصُونَ ٱللَّهَ مَآ أَمَرَهُمۡ وَيَفۡعَلُونَ مَا يُؤۡمَرُونَ

Ya ku waxanda suka yi imani, ku kare kawunanku da iyalanku daga wuta (wadda) makamashinta mutane ne da duwatsu, masu kula da ita mala’iku ne masu kaushin hali, masu tsananin gaske, ba sa sava wa Allah abin da Ya umarce su, suna kuma aikata abin da ake umartar su



Sura: Suratul Mulk

Aya : 6

وَلِلَّذِينَ كَفَرُواْ بِرَبِّهِمۡ عَذَابُ جَهَنَّمَۖ وَبِئۡسَ ٱلۡمَصِيرُ

Waxanda kuma suka kafirce wa Ubangijinsu suna da azabar Jahannama; makoma kuwa ta munana



Sura: Suratul Mulk

Aya : 7

إِذَآ أُلۡقُواْ فِيهَا سَمِعُواْ لَهَا شَهِيقٗا وَهِيَ تَفُورُ

Idan aka jefa su a cikinta sai su ji kururuwarta, tana tafarfasa



Sura: Suratul Mulk

Aya : 8

تَكَادُ تَمَيَّزُ مِنَ ٱلۡغَيۡظِۖ كُلَّمَآ أُلۡقِيَ فِيهَا فَوۡجٞ سَأَلَهُمۡ خَزَنَتُهَآ أَلَمۡ يَأۡتِكُمۡ نَذِيرٞ

Tana kusa da ta kekkece saboda tsananin fushi; duk sanda aka jefa wata tawaga a cikinta sai masu tsaron ta su tambaye su: “Shin mai gargaxi bai zo muku ba?”



Sura: Suratul Haqqa

Aya : 31

ثُمَّ ٱلۡجَحِيمَ صَلُّوهُ

Sannan ku shigar da shi (wutar) Jahimu



Sura: Suratul Haqqa

Aya : 32

ثُمَّ فِي سِلۡسِلَةٖ ذَرۡعُهَا سَبۡعُونَ ذِرَاعٗا فَٱسۡلُكُوهُ

Sannan ku sa shi cikin sarqa mai tsawo kamu saba’in



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 15

كَلَّآۖ إِنَّهَا لَظَىٰ

Faufau! Lalle ita (wutar) Laza ce



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 16

نَزَّاعَةٗ لِّلشَّوَىٰ

Mai xaxxaye fatar kai



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 17

تَدۡعُواْ مَنۡ أَدۡبَرَ وَتَوَلَّىٰ

Tana kiran wanda ya juya ya ba da baya



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 18

وَجَمَعَ فَأَوۡعَىٰٓ

Ya kuma tara (dukiya) sai ya voye (ta)



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 26

سَأُصۡلِيهِ سَقَرَ

(Allah ya ce): Da sannu zan shigar da shi (wutar) Saqara



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 27

وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا سَقَرُ

Me ya sanar da kai abin da ake ce wa Saqara?



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 28

لَا تُبۡقِي وَلَا تَذَرُ

Ba ta ragewa kuma ba ta barin (komai)



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 29

لَوَّاحَةٞ لِّلۡبَشَرِ

Mai xaxxaye fata ce



Sura: Suratul Insan

Aya : 4

إِنَّآ أَعۡتَدۡنَا لِلۡكَٰفِرِينَ سَلَٰسِلَاْ وَأَغۡلَٰلٗا وَسَعِيرًا

Lalle Mun tanadar wa kafirai sarqoqi da ququmai da wutar Sa’ira



Sura: Suratul Mursalat

Aya : 30

ٱنطَلِقُوٓاْ إِلَىٰ ظِلّٖ ذِي ثَلَٰثِ شُعَبٖ

Ku tafi zuwa wata inuwa mai rassa uku



Sura: Suratul Mursalat

Aya : 31

لَّا ظَلِيلٖ وَلَا يُغۡنِي مِنَ ٱللَّهَبِ

Ba mai ba da inuwa ba kuma ba mai karewa daga harshen wuta ba



Sura: Suratul Mursalat

Aya : 32

إِنَّهَا تَرۡمِي بِشَرَرٖ كَٱلۡقَصۡرِ

Haqiqa ita tana jefa tartsatsi kamar qaton gini



Sura: Suratul Mursalat

Aya : 33

كَأَنَّهُۥ جِمَٰلَتٞ صُفۡرٞ

Kai ka ce su raquma ne baqaqe



Sura: Suratun Naba’i

Aya : 21

إِنَّ جَهَنَّمَ كَانَتۡ مِرۡصَادٗا

Lalle Jahannama ta kasance madakata ce