Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 134

وَجَنَّـٰتٖ وَعُيُونٍ

“Da kuma gonakai da idanuwan ruwa



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 135

إِنِّيٓ أَخَافُ عَلَيۡكُمۡ عَذَابَ يَوۡمٍ عَظِيمٖ

“Lalle ni ina jiye muku tsoron azabar wani yini mai girma.”



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 136

قَالُواْ سَوَآءٌ عَلَيۡنَآ أَوَعَظۡتَ أَمۡ لَمۡ تَكُن مِّنَ ٱلۡوَٰعِظِينَ

Suka ce: “Mu duk xaya ne a wajenmu; ko ka yi wa’azi ko kuwa kada ka zamanto daga masu wa’azi



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 137

إِنۡ هَٰذَآ إِلَّا خُلُقُ ٱلۡأَوَّلِينَ

“Wannan ba wani abu ba ne in ban da halayyar mutanen farko



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 138

وَمَا نَحۡنُ بِمُعَذَّبِينَ

“Mu kuma ba waxanda za a yi wa azaba ba ne.”



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 139

فَكَذَّبُوهُ فَأَهۡلَكۡنَٰهُمۡۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ

Sai suka qaryata shi, sannan Muka hallaka su. Lalle a game da wannan tabbas akwai aya; kuma yawancinsu ba su zamanto muminai ba



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 140

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

Kuma lalle Ubangijinka tabbas Shi ne Mabuwayi, Mai jin qai



Sura: Suratul Ahqaf 

Aya : 21

۞وَٱذۡكُرۡ أَخَا عَادٍ إِذۡ أَنذَرَ قَوۡمَهُۥ بِٱلۡأَحۡقَافِ وَقَدۡ خَلَتِ ٱلنُّذُرُ مِنۢ بَيۡنِ يَدَيۡهِ وَمِنۡ خَلۡفِهِۦٓ أَلَّا تَعۡبُدُوٓاْ إِلَّا ٱللَّهَ إِنِّيٓ أَخَافُ عَلَيۡكُمۡ عَذَابَ يَوۡمٍ عَظِيمٖ

Ka kuma tuna xan’uwan Adawa (watau Hudu) lokacin da ya gargaxi mutanensa a al‑Ahqafu, alhali haqiqa masu gargaxi sun shuxe a gabaninsa da kuma a bayansa (suna cewa:) “Kada ku bauta wa (kowa) sai Allah, lalle ni ina jiye muku tsoron azabar wani yini mai girma.”



Sura: Suratul Ahqaf 

Aya : 22

قَالُوٓاْ أَجِئۡتَنَا لِتَأۡفِكَنَا عَنۡ ءَالِهَتِنَا فَأۡتِنَا بِمَا تَعِدُنَآ إِن كُنتَ مِنَ ٱلصَّـٰدِقِينَ

Sai suka ce: “Yanzu ka zo ne don ka kawar da mu daga ababen bautarmu? To ka zo mana da abin da kake yi mana alqawarin narko (da shi) idan ka kasance cikin masu gaskiya.”



Sura: Suratul Ahqaf 

Aya : 23

قَالَ إِنَّمَا ٱلۡعِلۡمُ عِندَ ٱللَّهِ وَأُبَلِّغُكُم مَّآ أُرۡسِلۡتُ بِهِۦ وَلَٰكِنِّيٓ أَرَىٰكُمۡ قَوۡمٗا تَجۡهَلُونَ

Sai ya ce: “Lalle sani yana wurin Allah kawai, ni kuma ina isar muku abin da aka aiko ni da shi ne, sai dai kuma ni ina ganin ku mutane ne masu wauta.”



Sura: Suratul Ahqaf 

Aya : 24

فَلَمَّا رَأَوۡهُ عَارِضٗا مُّسۡتَقۡبِلَ أَوۡدِيَتِهِمۡ قَالُواْ هَٰذَا عَارِضٞ مُّمۡطِرُنَاۚ بَلۡ هُوَ مَا ٱسۡتَعۡجَلۡتُم بِهِۦۖ رِيحٞ فِيهَا عَذَابٌ أَلِيمٞ

To lokacin da suka gan ta (azabar) wani hadari ne mai gindayawa, ya doso wa kwarurukansu sai suka ce: “Wannan hadari ne mai ba mu ruwa!” A’a, (ba ku sani ba) shi ne abin da kuke neman gaggautowarsa, watau iska da take cike da azaba mai raxaxi



Sura: Suratul Ahqaf 

Aya : 25

تُدَمِّرُ كُلَّ شَيۡءِۭ بِأَمۡرِ رَبِّهَا فَأَصۡبَحُواْ لَا يُرَىٰٓ إِلَّا مَسَٰكِنُهُمۡۚ كَذَٰلِكَ نَجۡزِي ٱلۡقَوۡمَ ٱلۡمُجۡرِمِينَ

Tana ruguza kowane irin abu da umarnin Ubangijinta, sai suka wayi gari ba abin da ake gani sai (kufaifan) gidajensu. Kamar haka Muke saka wa mutane masu manyan laifuka



Sura: Suratul Ahqaf 

Aya : 26

وَلَقَدۡ مَكَّنَّـٰهُمۡ فِيمَآ إِن مَّكَّنَّـٰكُمۡ فِيهِ وَجَعَلۡنَا لَهُمۡ سَمۡعٗا وَأَبۡصَٰرٗا وَأَفۡـِٔدَةٗ فَمَآ أَغۡنَىٰ عَنۡهُمۡ سَمۡعُهُمۡ وَلَآ أَبۡصَٰرُهُمۡ وَلَآ أَفۡـِٔدَتُهُم مِّن شَيۡءٍ إِذۡ كَانُواْ يَجۡحَدُونَ بِـَٔايَٰتِ ٱللَّهِ وَحَاقَ بِهِم مَّا كَانُواْ بِهِۦ يَسۡتَهۡزِءُونَ

Haqiqa Mun kafa su (a bayan qasa) kafawar da ba Mu yi muku irinta ba, Muka kuma sanya musu ji da gani da tunani, sai jin nasu da ganinsu da tunaninsu ba su amfana musu komai ba, tunda sun kasance suna musanta ayoyin Allah, abin da kuma suka kasance suna yi wa izgili ya auka musu