Sura: Suratul Haqqa

Aya : 25

وَأَمَّا مَنۡ أُوتِيَ كِتَٰبَهُۥ بِشِمَالِهِۦ فَيَقُولُ يَٰلَيۡتَنِي لَمۡ أُوتَ كِتَٰبِيَهۡ

Amma kuma wanda aka bai wa littafinsa a hannunsa na hagun sai ya ce: “Kaicona, ina ma da ba a ba ni littafina ba!



Sura: Suratul Haqqa

Aya : 26

وَلَمۡ أَدۡرِ مَا حِسَابِيَهۡ

“Kuma ban san mene ne sakamakona ba



Sura: Suratut Takwir

Aya : 8

وَإِذَا ٱلۡمَوۡءُۥدَةُ سُئِلَتۡ

Idan kuma yarinyar da aka binne da rai aka tambaye ta



Sura: Suratut Takwir

Aya : 9

بِأَيِّ ذَنۢبٖ قُتِلَتۡ

Da wane laifi ne aka kashe ta?



Sura: Suratul Inshiqaq

Aya : 7

فَأَمَّا مَنۡ أُوتِيَ كِتَٰبَهُۥ بِيَمِينِهِۦ

To amma duk wanda aka bai wa littafinsa a hannunsa na dama



Sura: Suratul Inshiqaq

Aya : 8

فَسَوۡفَ يُحَاسَبُ حِسَابٗا يَسِيرٗا

To za a yi masa hisabi mai sauqi[1]


1- Watau ta hanyar bijiro ayyukansa a dunqule ba tare da binciken qwaqwaf ba.


Sura: Suratul Ghashiya

Aya : 26

ثُمَّ إِنَّ عَلَيۡنَا حِسَابَهُم

Sannan kuma a kanmu ne hisabinsu yake



Sura: Suratut Takasur

Aya : 8

ثُمَّ لَتُسۡـَٔلُنَّ يَوۡمَئِذٍ عَنِ ٱلنَّعِيمِ

Sannan kuma tabbas lalle za a tambaye ku a wannan ranar game da ni’imomin (da kuka mora a duniya)