Sura: Suratu Ali-Imran

Aya : 14

زُيِّنَ لِلنَّاسِ حُبُّ ٱلشَّهَوَٰتِ مِنَ ٱلنِّسَآءِ وَٱلۡبَنِينَ وَٱلۡقَنَٰطِيرِ ٱلۡمُقَنطَرَةِ مِنَ ٱلذَّهَبِ وَٱلۡفِضَّةِ وَٱلۡخَيۡلِ ٱلۡمُسَوَّمَةِ وَٱلۡأَنۡعَٰمِ وَٱلۡحَرۡثِۗ ذَٰلِكَ مَتَٰعُ ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَاۖ وَٱللَّهُ عِندَهُۥ حُسۡنُ ٱلۡمَـَٔابِ

An qawata wa mutane son sha’awace-sha’awace na mata da ‘ya’ya da dukiya mai yawa abar tarawa ta zinariya da azurfa da kuma kiwatattun dawaki da dabbobi na gida da amfanin gona. Waxannan duk morewa ce ta rayuwar duniya; Allah kuwa a wurinsa ne kyakkyawar makoma take



Sura: Suratun Nisa’i

Aya : 28

يُرِيدُ ٱللَّهُ أَن يُخَفِّفَ عَنكُمۡۚ وَخُلِقَ ٱلۡإِنسَٰنُ ضَعِيفٗا

Allah Yana nufin Ya sassauta muku. Kuma an halicci xan’adam mai rauni ne



Sura: Suratu Yunus

Aya : 12

وَإِذَا مَسَّ ٱلۡإِنسَٰنَ ٱلضُّرُّ دَعَانَا لِجَنۢبِهِۦٓ أَوۡ قَاعِدًا أَوۡ قَآئِمٗا فَلَمَّا كَشَفۡنَا عَنۡهُ ضُرَّهُۥ مَرَّ كَأَن لَّمۡ يَدۡعُنَآ إِلَىٰ ضُرّٖ مَّسَّهُۥۚ كَذَٰلِكَ زُيِّنَ لِلۡمُسۡرِفِينَ مَا كَانُواْ يَعۡمَلُونَ

Idan kuma wata cuta ta sami mutum, sai ya roqe Mu, a kishingixe ne ko a zaune ko kuwa a tsaye. To lokacin da Muka yaye masa cutarsa sai ya ci gaba (da halinsa) kamar bai tava roqon Mu game da wata cuta da ta shafe shi ba. Kamar haka ne aka qawata wa mavarnata abin da suka kasance suna aikatawa



Sura: Suratu Yunus

Aya : 44

إِنَّ ٱللَّهَ لَا يَظۡلِمُ ٱلنَّاسَ شَيۡـٔٗا وَلَٰكِنَّ ٱلنَّاسَ أَنفُسَهُمۡ يَظۡلِمُونَ

Lalle Allah ba Ya zaluntar mutane da komai, sai dai mutane kawunansu kawai suke zalunta



Sura: Suratu Hud

Aya : 9

وَلَئِنۡ أَذَقۡنَا ٱلۡإِنسَٰنَ مِنَّا رَحۡمَةٗ ثُمَّ نَزَعۡنَٰهَا مِنۡهُ إِنَّهُۥ لَيَـُٔوسٞ كَفُورٞ

Kuma tabbas idan Muka xanxana wa mutum wata rahama daga gare Mu sannan Muka karve ta daga gare shi, lalle shi mai yawan yanke qauna ne, mai kuma yawan kafirci



Sura: Suratu Hud

Aya : 10

وَلَئِنۡ أَذَقۡنَٰهُ نَعۡمَآءَ بَعۡدَ ضَرَّآءَ مَسَّتۡهُ لَيَقُولَنَّ ذَهَبَ ٱلسَّيِّـَٔاتُ عَنِّيٓۚ إِنَّهُۥ لَفَرِحٞ فَخُورٌ

Lalle kuma idan Muka xanxana masa daxi bayan ya sha wahala da ta same shi, tabbas zai riqa cewa: “Ai munanan (abubuwa) sun bar ni.” Lalle shi mai farin ciki ne mai yawan alfahari



Sura: Suratu Hud

Aya : 11

إِلَّا ٱلَّذِينَ صَبَرُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ أُوْلَـٰٓئِكَ لَهُم مَّغۡفِرَةٞ وَأَجۡرٞ كَبِيرٞ

Sai dai waxanda suka yi haquri suka kuma yi aiki nagari, waxannan suna da gafara da kuma lada mai girma



Sura: Suratu Yusuf 

Aya : 38

وَٱتَّبَعۡتُ مِلَّةَ ءَابَآءِيٓ إِبۡرَٰهِيمَ وَإِسۡحَٰقَ وَيَعۡقُوبَۚ مَا كَانَ لَنَآ أَن نُّشۡرِكَ بِٱللَّهِ مِن شَيۡءٖۚ ذَٰلِكَ مِن فَضۡلِ ٱللَّهِ عَلَيۡنَا وَعَلَى ٱلنَّاسِ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَ ٱلنَّاسِ لَا يَشۡكُرُونَ

“Na kuma bi hanyar iyayena Ibrahimu da Is’haqa da kuma Yaqubu. Bai kamace mu ba a ce mu tara wani abu da Allah. Wannan yana daga falalar Allah a gare mu da kuma sauran mutane, sai dai kuma yawancin mutane ba sa godewa



Sura: Suratur Ra’ad

Aya : 1

الٓمٓرۚ تِلۡكَ ءَايَٰتُ ٱلۡكِتَٰبِۗ وَٱلَّذِيٓ أُنزِلَ إِلَيۡكَ مِن رَّبِّكَ ٱلۡحَقُّ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَ ٱلنَّاسِ لَا يُؤۡمِنُونَ

ALIF LAM MIM RA[1]. Waxannan ayoyi ne na Littafi (wato Alqur’ani). Wanda kuma aka saukar maka daga Ubangijinka gaskiya ne, sai dai lalle yawancin mutane ba sa yin imani


1- Duba Suratul Baqara, aya ta 1, hashiya ta 8.


Sura: Suratul Isra’i

Aya : 11

وَيَدۡعُ ٱلۡإِنسَٰنُ بِٱلشَّرِّ دُعَآءَهُۥ بِٱلۡخَيۡرِۖ وَكَانَ ٱلۡإِنسَٰنُ عَجُولٗا

Kuma mutum yakan roqi sharri[1] kamar yadda yake roqon alheri; mutum kuwa ya zamanto mai gaggawa ne


1- Watau idan ya yi fushi yakan yi wa kansa ko ‘ya’yansa ko dukiyarsa mummunar addu’a.


Sura: Suratul Isra’i

Aya : 67

وَإِذَا مَسَّكُمُ ٱلضُّرُّ فِي ٱلۡبَحۡرِ ضَلَّ مَن تَدۡعُونَ إِلَّآ إِيَّاهُۖ فَلَمَّا نَجَّىٰكُمۡ إِلَى ٱلۡبَرِّ أَعۡرَضۡتُمۡۚ وَكَانَ ٱلۡإِنسَٰنُ كَفُورًا

Idan kuma bala’i ya same ku a cikin kogi sai duk waxanda kuke kira su vace (muku) sai Shi kawai; sannan lokacin da Ya tserar da ku zuwa sarari sai kuka bijire. Kai mutum ya tabbata butulu!



Sura: Suratul Isra’i

Aya : 100

قُل لَّوۡ أَنتُمۡ تَمۡلِكُونَ خَزَآئِنَ رَحۡمَةِ رَبِّيٓ إِذٗا لَّأَمۡسَكۡتُمۡ خَشۡيَةَ ٱلۡإِنفَاقِۚ وَكَانَ ٱلۡإِنسَٰنُ قَتُورٗا

Ka ce da su: “Idan da ku ne kuka mallaki taskokin rahamar Ubangijina to lalle da kun riqe su qam-qam don tsoron ciyarwa. Mutum kuwa ya tabbata mai tsananin rowa ne



Sura: Suratul Kahf 

Aya : 54

وَلَقَدۡ صَرَّفۡنَا فِي هَٰذَا ٱلۡقُرۡءَانِ لِلنَّاسِ مِن كُلِّ مَثَلٖۚ وَكَانَ ٱلۡإِنسَٰنُ أَكۡثَرَ شَيۡءٖ جَدَلٗا

Kuma haqiqa Mun sassarafa kowane irin misali ga mutane a cikin wannan Alqur’anin. Mutum kuwa ya kasance wanda ya fi komai yawan musu



Sura: Suratul Anbiya

Aya : 37

خُلِقَ ٱلۡإِنسَٰنُ مِنۡ عَجَلٖۚ سَأُوْرِيكُمۡ ءَايَٰتِي فَلَا تَسۡتَعۡجِلُونِ

An halicci mutum da son gaggawa. Ba da daxewa ba zan nuna muku ayoyina, to don haka kada ku nemi gaggauto da (zuwansu)



Sura: Suratul Ahzab

Aya : 72

إِنَّا عَرَضۡنَا ٱلۡأَمَانَةَ عَلَى ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَٱلۡجِبَالِ فَأَبَيۡنَ أَن يَحۡمِلۡنَهَا وَأَشۡفَقۡنَ مِنۡهَا وَحَمَلَهَا ٱلۡإِنسَٰنُۖ إِنَّهُۥ كَانَ ظَلُومٗا جَهُولٗا

Lalle Mun bijiro da amana[1] ga sammai da qasa da duwatsu sai suka qi xaukar ta suka ji tsoron ta, sai kuwa mutum ya xauke ta; lalle shi (mutum) ya kasance mai zaluntar kansa ne, mai jahilci


1- Amana a nan, su ne dokokin shari’a na umarni da hani.


Sura: Suratuz Zumar

Aya : 49

فَإِذَا مَسَّ ٱلۡإِنسَٰنَ ضُرّٞ دَعَانَا ثُمَّ إِذَا خَوَّلۡنَٰهُ نِعۡمَةٗ مِّنَّا قَالَ إِنَّمَآ أُوتِيتُهُۥ عَلَىٰ عِلۡمِۭۚ بَلۡ هِيَ فِتۡنَةٞ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَهُمۡ لَا يَعۡلَمُونَ

To idan wata cuta ta samu mutum sai ya roqe Mu, sannan idan Mun ba shi wata ni’ima daga gare Mu sai ya ce: “Ai an ba ni ita ne kawai don sanin (cancantata)”. Ba haka ba ne, ita wata jarrabawa ce kawai, sai dai yawancinsu ba sa sanin (haka)



Sura: Suratu Ghafir

Aya : 61

ٱللَّهُ ٱلَّذِي جَعَلَ لَكُمُ ٱلَّيۡلَ لِتَسۡكُنُواْ فِيهِ وَٱلنَّهَارَ مُبۡصِرًاۚ إِنَّ ٱللَّهَ لَذُو فَضۡلٍ عَلَى ٱلنَّاسِ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَ ٱلنَّاسِ لَا يَشۡكُرُونَ

Allah ne wanda Ya halitta muku dare don ku natsu a cikinsa, rana kuma don ku ga (yadda za ku yi harka). Lalle Allah Mai falala ne ga mutane, sai dai kuma yawancinsu ba sa godewa



Sura: Suratu Fussilat

Aya : 49

لَّا يَسۡـَٔمُ ٱلۡإِنسَٰنُ مِن دُعَآءِ ٱلۡخَيۡرِ وَإِن مَّسَّهُ ٱلشَّرُّ فَيَـُٔوسٞ قَنُوطٞ

Mutum ba ya qosawa wajen roqon alheri, idan kuwa wani sharri ya same shi, to sai ya zama mai tsananin xebe qauna



Sura: Suratu Fussilat

Aya : 50

وَلَئِنۡ أَذَقۡنَٰهُ رَحۡمَةٗ مِّنَّا مِنۢ بَعۡدِ ضَرَّآءَ مَسَّتۡهُ لَيَقُولَنَّ هَٰذَا لِي وَمَآ أَظُنُّ ٱلسَّاعَةَ قَآئِمَةٗ وَلَئِن رُّجِعۡتُ إِلَىٰ رَبِّيٓ إِنَّ لِي عِندَهُۥ لَلۡحُسۡنَىٰۚ فَلَنُنَبِّئَنَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ بِمَا عَمِلُواْ وَلَنُذِيقَنَّهُم مِّنۡ عَذَابٍ غَلِيظٖ

Tabbas kuma idan Muka xanxana masa wata rahama tamu bayan wata cuta da ta same shi, tabbas zai riqa cewa: “Wannan nawa ne, kuma ba na tsammanin alqiyama za ta tashi, kuma tabbas idan ma da za a mayar da ni zuwa ga Ubangijina, lalle zan zama mai samun mafi kyan sakamako a wurinsa.” To tabbas za Mu saka wa waxanda suka kafirta da abin da suka aikata, kuma tabbas za Mu xanxana musu azaba mai gwavi



Sura: Suratu Fussilat

Aya : 51

وَإِذَآ أَنۡعَمۡنَا عَلَى ٱلۡإِنسَٰنِ أَعۡرَضَ وَنَـَٔا بِجَانِبِهِۦ وَإِذَا مَسَّهُ ٱلشَّرُّ فَذُو دُعَآءٍ عَرِيضٖ

Idan kuma Muka yi wa mutum ni’ima sai ya bijire ya ja jikinsa nesa (daga tuna Allah), kuma idan sharri ya same shi, sai ya zama mai faffaxar addu’a



Sura: Suratus Shura

Aya : 48

فَإِنۡ أَعۡرَضُواْ فَمَآ أَرۡسَلۡنَٰكَ عَلَيۡهِمۡ حَفِيظًاۖ إِنۡ عَلَيۡكَ إِلَّا ٱلۡبَلَٰغُۗ وَإِنَّآ إِذَآ أَذَقۡنَا ٱلۡإِنسَٰنَ مِنَّا رَحۡمَةٗ فَرِحَ بِهَاۖ وَإِن تُصِبۡهُمۡ سَيِّئَةُۢ بِمَا قَدَّمَتۡ أَيۡدِيهِمۡ فَإِنَّ ٱلۡإِنسَٰنَ كَفُورٞ

To idan sun bijire, to ba Mu aika ka don ka zama mai gadin su ba; ba abin da yake kanka sai isar da saqo. Lalle kuma Mu idan Muka xanxana wa mutum wata rahama daga gare Mu sai ya riqa tutiya da ita. Idan kuma wani mummunan abu ya same su saboda abin da hannayensu suka aikata, to lalle shi mutum butulu ne



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 19

۞إِنَّ ٱلۡإِنسَٰنَ خُلِقَ هَلُوعًا

Lalle mutum an halicce shi mai rashin nutsuwa ne



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 20

إِذَا مَسَّهُ ٱلشَّرُّ جَزُوعٗا

(Watau) idan sharri ya same shi ya zama mai raki



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 21

وَإِذَا مَسَّهُ ٱلۡخَيۡرُ مَنُوعًا

Idan kuma alheri ya same shi ya zama mai maqo



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 22

إِلَّا ٱلۡمُصَلِّينَ

Sai dai masallata



Sura: Suratul Fajr

Aya : 15

فَأَمَّا ٱلۡإِنسَٰنُ إِذَا مَا ٱبۡتَلَىٰهُ رَبُّهُۥ فَأَكۡرَمَهُۥ وَنَعَّمَهُۥ فَيَقُولُ رَبِّيٓ أَكۡرَمَنِ

Amma kuma mutum idan Ubangijinsa Ya jarrabe shi sai Ya karrama shi, Ya kuma yi masa ni’ima, sai ya ce: “Ubangijina Ya karrama ni.”



Sura: Suratul Fajr

Aya : 16

وَأَمَّآ إِذَا مَا ٱبۡتَلَىٰهُ فَقَدَرَ عَلَيۡهِ رِزۡقَهُۥ فَيَقُولُ رَبِّيٓ أَهَٰنَنِ

Amma kuma idan Ya jarrabe shi sai Ya quntata masa a arzikinsa, sai ya ce: “Ubangijina Ya wulaqanta ni.”



Sura: Suratul Fajr

Aya : 20

وَتُحِبُّونَ ٱلۡمَالَ حُبّٗا جَمّٗا

Kuma kuna son dukiya so mai yawa



Sura: Suratut Tin

Aya : 4

لَقَدۡ خَلَقۡنَا ٱلۡإِنسَٰنَ فِيٓ أَحۡسَنِ تَقۡوِيمٖ

Haqiqa Mun halicci mutum a kan mafi kyan diri



Sura: Suratul Alaq

Aya : 6

كَلَّآ إِنَّ ٱلۡإِنسَٰنَ لَيَطۡغَىٰٓ

Tabbas! Lalle (jinsin) mutum haqiqa yana yin xagawa