Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 18

قَالَ هِيَ عَصَايَ أَتَوَكَّؤُاْ عَلَيۡهَا وَأَهُشُّ بِهَا عَلَىٰ غَنَمِي وَلِيَ فِيهَا مَـَٔارِبُ أُخۡرَىٰ

(Musa) ya ce: “Ai sandata ce da nake jingina a kanta, ina kuma kaxo wa dabbobina ganye da ita, ina kuma da sauran wasu buqatu game da ita.”



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 19

قَالَ أَلۡقِهَا يَٰمُوسَىٰ

(Allah) Ya ce: “Jefar da ita ya Musa.”



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 20

فَأَلۡقَىٰهَا فَإِذَا هِيَ حَيَّةٞ تَسۡعَىٰ

Sai ya jefar da ita, sai ga ta ta zama macijiya tana ta sauri



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 21

قَالَ خُذۡهَا وَلَا تَخَفۡۖ سَنُعِيدُهَا سِيرَتَهَا ٱلۡأُولَىٰ

Ya ce: “Kama ta, kuma kada ka ji tsoro; za Mu mai da ita kamar yadda take a da



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 22

وَٱضۡمُمۡ يَدَكَ إِلَىٰ جَنَاحِكَ تَخۡرُجۡ بَيۡضَآءَ مِنۡ غَيۡرِ سُوٓءٍ ءَايَةً أُخۡرَىٰ

“Kuma ka haxa hannunka da kwivinka zai fito fari sal ba tare da wata cuta ba; (wannan) wata ayar ce daban



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 23

لِنُرِيَكَ مِنۡ ءَايَٰتِنَا ٱلۡكُبۡرَى

“Domin Mu nuna maka irin manya-manyan ayoyinmu



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 24

ٱذۡهَبۡ إِلَىٰ فِرۡعَوۡنَ إِنَّهُۥ طَغَىٰ

“Ka tafi wurin Fir’auna don kuwa lalle ya qetare iyaka.”



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 25

قَالَ رَبِّ ٱشۡرَحۡ لِي صَدۡرِي

(Musa) ya ce: “Ubangijina Ka buxe mini qirjina[1]


1- Watau ya cire masa in’ina da take damun sa.


Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 26

وَيَسِّرۡ لِيٓ أَمۡرِي

“Kuma Ka sauqaqa mini lamarina



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 27

وَٱحۡلُلۡ عُقۡدَةٗ مِّن لِّسَانِي

“Ka kuma warware qullin da yake a harshena



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 28

يَفۡقَهُواْ قَوۡلِي

“(Don) su fahimci maganata



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 29

وَٱجۡعَل لِّي وَزِيرٗا مِّنۡ أَهۡلِي

“Kuma Ka sanya mini waziri daga dangina



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 30

هَٰرُونَ أَخِي

“(Watau) xau’uwana Haruna



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 31

ٱشۡدُدۡ بِهِۦٓ أَزۡرِي

“Ka qarfafa gwiwata da shi



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 32

وَأَشۡرِكۡهُ فِيٓ أَمۡرِي

“Kuma Ka shigar da shi cikin lamarina[1]


1- Watau shi ma ya ba shi annabta ya aiko su tare.


Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 33

كَيۡ نُسَبِّحَكَ كَثِيرٗا

“Domin mu tsarkake Ka da yawa



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 34

وَنَذۡكُرَكَ كَثِيرًا

“Mu kuma ambace Ka da yawa



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 35

إِنَّكَ كُنتَ بِنَا بَصِيرٗا

“Lalle Kai Ka kasance Kana ganin mu.”



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 36

قَالَ قَدۡ أُوتِيتَ سُؤۡلَكَ يَٰمُوسَىٰ

(Allah) Ya ce: “Haqiqa an ba ka abin da ka tambaya, ya Musa



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 37

وَلَقَدۡ مَنَنَّا عَلَيۡكَ مَرَّةً أُخۡرَىٰٓ

“Haqiqa kuma Mun yi ni’ima a gare ka a wani lokaci



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 38

إِذۡ أَوۡحَيۡنَآ إِلَىٰٓ أُمِّكَ مَا يُوحَىٰٓ

“Sanda Muka yiwo wahayi ga mahaifiyarka da abin da ake yin wahayi da shi



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 39

أَنِ ٱقۡذِفِيهِ فِي ٱلتَّابُوتِ فَٱقۡذِفِيهِ فِي ٱلۡيَمِّ فَلۡيُلۡقِهِ ٱلۡيَمُّ بِٱلسَّاحِلِ يَأۡخُذۡهُ عَدُوّٞ لِّي وَعَدُوّٞ لَّهُۥۚ وَأَلۡقَيۡتُ عَلَيۡكَ مَحَبَّةٗ مِّنِّي وَلِتُصۡنَعَ عَلَىٰ عَيۡنِيٓ

“Cewa, ‘ki saka shi (jinjirin) a cikin akwatu, sannan ki jefa shi cikin kogi, to sai kogin ya jefa shi a gava, sai maqiyina kuma maqiyinsa ya xauke shi.’ Na kuma sanya maka farin jini daga gare Ni, don kuma a yi tarbiyar ka a gaban idona



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 40

إِذۡ تَمۡشِيٓ أُخۡتُكَ فَتَقُولُ هَلۡ أَدُلُّكُمۡ عَلَىٰ مَن يَكۡفُلُهُۥۖ فَرَجَعۡنَٰكَ إِلَىٰٓ أُمِّكَ كَيۡ تَقَرَّ عَيۡنُهَا وَلَا تَحۡزَنَۚ وَقَتَلۡتَ نَفۡسٗا فَنَجَّيۡنَٰكَ مِنَ ٱلۡغَمِّ وَفَتَنَّـٰكَ فُتُونٗاۚ فَلَبِثۡتَ سِنِينَ فِيٓ أَهۡلِ مَدۡيَنَ ثُمَّ جِئۡتَ عَلَىٰ قَدَرٖ يَٰمُوسَىٰ

“Lokacin da ‘yar’uwarka take tafiya tana cewa (da su): ‘Yanzu ba na haxa ku da wadda za ta raine shi ba?’ Sai Muka komo da kai zuwa ga mahaifiyarka don zuciyarta ta yi sanyi, kada kuma ta yi baqin ciki. Kuma ka kashe wani mutum[1] sannan Muka tserar da kai daga uquba, Muka kuma jarrabe ka da jarrabobi daban-daban. Sannan ka zauna shekaru a cikin mutanen Madyana, sannan ka zo (nan) daidai lokacin da Na qadarta (maka annabta) ya Musa


1- Shi ne Baqibxen da Annabi Musa ya naushe shi ya faxi nan take ya mutu.


Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 41

وَٱصۡطَنَعۡتُكَ لِنَفۡسِي

“Kuma Na zave ka don kaina[1]


1- Watau Allah () ya zave shi domin ya yi magana da shi, ya aika shi zuwa Fir’auna da mutanensa.


Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 42

ٱذۡهَبۡ أَنتَ وَأَخُوكَ بِـَٔايَٰتِي وَلَا تَنِيَا فِي ذِكۡرِي

“Ka tafi kai da xan’uwanka da ayoyina, kada kuwa ku sassauta game da ambatona



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 43

ٱذۡهَبَآ إِلَىٰ فِرۡعَوۡنَ إِنَّهُۥ طَغَىٰ

“Ku tafi wurin Fir’auna, don ko lalle ya wuce iyaka



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 44

فَقُولَا لَهُۥ قَوۡلٗا لَّيِّنٗا لَّعَلَّهُۥ يَتَذَكَّرُ أَوۡ يَخۡشَىٰ

“Sai ku gaya masa magana mai taushi, ko wataqila zai wa’azantu ko kuma ya ji tsoron (azabar Allah).”



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 45

قَالَا رَبَّنَآ إِنَّنَا نَخَافُ أَن يَفۡرُطَ عَلَيۡنَآ أَوۡ أَن يَطۡغَىٰ

(Musa da Haruna) suka ce: “Ya Ubangijinmu, lalle mu muna tsoron ya far mana ko kuma ya wuce iyaka (wajen yi mana uquba).”



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 46

قَالَ لَا تَخَافَآۖ إِنَّنِي مَعَكُمَآ أَسۡمَعُ وَأَرَىٰ

Ya ce: “Kada ku ji tsoro; haqiqa Ni ina tare da ku, ina ji kuma ina ganin (komai)



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 47

فَأۡتِيَاهُ فَقُولَآ إِنَّا رَسُولَا رَبِّكَ فَأَرۡسِلۡ مَعَنَا بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ وَلَا تُعَذِّبۡهُمۡۖ قَدۡ جِئۡنَٰكَ بِـَٔايَةٖ مِّن رَّبِّكَۖ وَٱلسَّلَٰمُ عَلَىٰ مَنِ ٱتَّبَعَ ٱلۡهُدَىٰٓ

“Sai ku tafi wajensa sannan ku ce (da shi): “Lalle mu manzannin Ubangijinka ne, sai ka sakar mana Banu-Isra’ila, kada kuma ka azabtar da su; haqiqa mun zo maka da aya daga Ubangijinka; aminci kuwa ya tabbata ga wanda ya bi shiriya