Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 12

قَالَ رَبِّ إِنِّيٓ أَخَافُ أَن يُكَذِّبُونِ

(Musa) ya ce: “Ya Ubangijina, lalle ni ina tsoron su qaryata ni



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 13

وَيَضِيقُ صَدۡرِي وَلَا يَنطَلِقُ لِسَانِي فَأَرۡسِلۡ إِلَىٰ هَٰرُونَ

“Kuma qirjina yana quntata, kuma harshena ba ya sakuwa, sai Ka aika zuwa ga (xan’uwana) Haruna



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 14

وَلَهُمۡ عَلَيَّ ذَنۢبٞ فَأَخَافُ أَن يَقۡتُلُونِ

“Ni kuma akwai wani laifi da na yi musu, sai nake tsoron su kashe ni.”



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 15

قَالَ كَلَّاۖ فَٱذۡهَبَا بِـَٔايَٰتِنَآۖ إِنَّا مَعَكُم مُّسۡتَمِعُونَ

(Allah) Ya ce: “A’a; (ba abin da zai same ka), sai ku tafi (kai da xan’uwanka) da ayoyinmu; lalle Mu masu jin (komai da zai faru) ne tare da ku



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 16

فَأۡتِيَا فِرۡعَوۡنَ فَقُولَآ إِنَّا رَسُولُ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

“Ku je wajen Fir’auna sai ku faxa masa cewa: ‘Lalle mu manzannin Ubangijin talikai ne



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 17

أَنۡ أَرۡسِلۡ مَعَنَا بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ

“‘Cewa, ka sako mana da Banu-Isra’ila’.”



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 18

قَالَ أَلَمۡ نُرَبِّكَ فِينَا وَلِيدٗا وَلَبِثۡتَ فِينَا مِنۡ عُمُرِكَ سِنِينَ

(Fir’auna) ya ce: “Yanzu ba mu muka raine ka a cikinmu tun kana jariri ba, kuma ka zauna ka yi wasu shekaru na rayuwarka a cikinmu?



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 19

وَفَعَلۡتَ فَعۡلَتَكَ ٱلَّتِي فَعَلۡتَ وَأَنتَ مِنَ ٱلۡكَٰفِرِينَ

“Ka kuma aikata aika-aikarka da ka aikata[1] alhali kuwa kana daga masu butulce wa (ni’imata)?”


1- Yana nufin kashe Baqibxe da ya yi lokacin da ya same shi yana faxa da Ba’isra’ile. Duba Suratul Qasas, ayat ta 15.


Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 20

قَالَ فَعَلۡتُهَآ إِذٗا وَأَنَا۠ مِنَ ٱلضَّآلِّينَ

(Musa) ya ce: “Na aikata haka ne a lokacin ina cikin marasa shiriya (ta rashin wahayi)



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 21

فَفَرَرۡتُ مِنكُمۡ لَمَّا خِفۡتُكُمۡ فَوَهَبَ لِي رَبِّي حُكۡمٗا وَجَعَلَنِي مِنَ ٱلۡمُرۡسَلِينَ

“Sannan na guje muku lokacin da na tsorata da ku, sai Ubangijina Ya ba ni kyautar ilimi Ya kuma sanya ni daga manzanni



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 22

وَتِلۡكَ نِعۡمَةٞ تَمُنُّهَا عَلَيَّ أَنۡ عَبَّدتَّ بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ

“Waccen ni’imar kuwa da kake goranta min ita saboda ka bautar da Bani-Isra’ila ne.”



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 23

قَالَ فِرۡعَوۡنُ وَمَا رَبُّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Fir’auna ya ce: “To wane ne Ubangijin talikai?”



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 24

قَالَ رَبُّ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا بَيۡنَهُمَآۖ إِن كُنتُم مُّوقِنِينَ

(Musa) ya ce: “(Shi ne) Ubangijin sammai da qasa da abin da yake tsakaninsu, idan har kun kasance masu sakankancewa (da hakan)”



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 25

قَالَ لِمَنۡ حَوۡلَهُۥٓ أَلَا تَسۡتَمِعُونَ

(Fir’auna) ya ce da waxanda suke kewaye da shi: “Shin ba kwa jin (abin da yake faxa)?”



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 26

قَالَ رَبُّكُمۡ وَرَبُّ ءَابَآئِكُمُ ٱلۡأَوَّلِينَ

(Musa) ya ce: “Shi ne Ubangijinku kuma Ubangijin iyayenku na farko!”



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 27

قَالَ إِنَّ رَسُولَكُمُ ٱلَّذِيٓ أُرۡسِلَ إِلَيۡكُمۡ لَمَجۡنُونٞ

(Fir’auna) ya ce: “Lalle Manzon da aka aiko muku tabbas mai tavin hankali ne!”



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 28

قَالَ رَبُّ ٱلۡمَشۡرِقِ وَٱلۡمَغۡرِبِ وَمَا بَيۡنَهُمَآۖ إِن كُنتُمۡ تَعۡقِلُونَ

(Musa) ya ce: “(Shi ne) Ubangijin mahudar rana da mafaxarta da kuma abin da yake tsakaninsu; in kun zamanto masu hankalta.”



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 29

قَالَ لَئِنِ ٱتَّخَذۡتَ إِلَٰهًا غَيۡرِي لَأَجۡعَلَنَّكَ مِنَ ٱلۡمَسۡجُونِينَ

(Fir’auna) ya ce: “Na rantse in har ka riqi wani abin bauta ba ni ba, tabbas zan jefa ka cikin ‘yan kurkuku!”



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 30

قَالَ أَوَلَوۡ جِئۡتُكَ بِشَيۡءٖ مُّبِينٖ

(Musa) ya ce: “Ko da na zo maka da wani abu bayyananne?”



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 31

قَالَ فَأۡتِ بِهِۦٓ إِن كُنتَ مِنَ ٱلصَّـٰدِقِينَ

(Fir’auna) ya ce: “To ka zo da shi xin in ka kasance daga masu gaskiya.”



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 32

فَأَلۡقَىٰ عَصَاهُ فَإِذَا هِيَ ثُعۡبَانٞ مُّبِينٞ

Sannan (Musa) ya jefa sandarsa sai ga ta (ta zama) kumurci quru-quru



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 33

وَنَزَعَ يَدَهُۥ فَإِذَا هِيَ بَيۡضَآءُ لِلنَّـٰظِرِينَ

Ya kuma zaro hannunsa (daga cikin rigarsa) sai ga shi fari fat ga masu gani



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 34

قَالَ لِلۡمَلَإِ حَوۡلَهُۥٓ إِنَّ هَٰذَا لَسَٰحِرٌ عَلِيمٞ

(Sai Fir’auna) ya ce da manyan mutanen da ke kewaye da shi: “Lalle wannan tabbas mai sihiri ne qwararre



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 35

يُرِيدُ أَن يُخۡرِجَكُم مِّنۡ أَرۡضِكُم بِسِحۡرِهِۦ فَمَاذَا تَأۡمُرُونَ

“Yana nufi ne ya fitar da ku daga qasarku da sihirinsa, to da me za ku yi umarni?”



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 36

قَالُوٓاْ أَرۡجِهۡ وَأَخَاهُ وَٱبۡعَثۡ فِي ٱلۡمَدَآئِنِ حَٰشِرِينَ

Suka ce: “Ka dakatar da shi tare da xan’uwansa, kuma ka aika manzanni cikin birane su tattaro maka (masu sihiri)



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 37

يَأۡتُوكَ بِكُلِّ سَحَّارٍ عَلِيمٖ

“Su zo maka da duk wani mai sihiri qwararre.”



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 38

فَجُمِعَ ٱلسَّحَرَةُ لِمِيقَٰتِ يَوۡمٖ مَّعۡلُومٖ

Sai aka tattara masu sihirin (don su zo) a qayyadajjiyar rana sananniya[1]


1- Watau ranar bikin idinsu.


Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 39

وَقِيلَ لِلنَّاسِ هَلۡ أَنتُم مُّجۡتَمِعُونَ

Aka kuma ce da mutane: “Shin za ku tattaru



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 40

لَعَلَّنَا نَتَّبِعُ ٱلسَّحَرَةَ إِن كَانُواْ هُمُ ٱلۡغَٰلِبِينَ

“Don mu goyi bayan masu sihiri idan har sun kasance su ne masu galaba?”



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 41

فَلَمَّا جَآءَ ٱلسَّحَرَةُ قَالُواْ لِفِرۡعَوۡنَ أَئِنَّ لَنَا لَأَجۡرًا إِن كُنَّا نَحۡنُ ٱلۡغَٰلِبِينَ

Sannan lokacin da masu sihirin suka zo sai suka ce da Fir’auna: “Shin muna da wani lada (da za ka ba mu) in har mun zama mu ne masu galaba?”