Sura: Suratu Qaf 

Aya : 45

نَّحۡنُ أَعۡلَمُ بِمَا يَقُولُونَۖ وَمَآ أَنتَ عَلَيۡهِم بِجَبَّارٖۖ فَذَكِّرۡ بِٱلۡقُرۡءَانِ مَن يَخَافُ وَعِيدِ

Mu ne Muka fi sanin abin da (kafiran Makka) suke faxa; kuma kai ba mai tilasta musu ba ne; saboda haka sai ka yi wa’azi da Alqur’ani ga wanda yake tsoron azabata



Sura: Suratuz Zariyat

Aya : 55

وَذَكِّرۡ فَإِنَّ ٱلذِّكۡرَىٰ تَنفَعُ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ

Kuma ka yi wa’azi, don ko lalle wa’azi yana amfanar muminai



Sura: Suratux Xur

Aya : 48

وَٱصۡبِرۡ لِحُكۡمِ رَبِّكَ فَإِنَّكَ بِأَعۡيُنِنَاۖ وَسَبِّحۡ بِحَمۡدِ رَبِّكَ حِينَ تَقُومُ

Kuma ka yi haquri da hukuncin Ubangijika, don ko lalle kana qarqashin lurarmu; kuma ka yi tasbihi da yabon Ubangijinka lokacin da za ka tashi (daga bacci)



Sura: Suratux Xur

Aya : 49

وَمِنَ ٱلَّيۡلِ فَسَبِّحۡهُ وَإِدۡبَٰرَ ٱلنُّجُومِ

Da daddare kuma sai ka tsarkake Shi da kuma lokacin da taurari suka ba da baya



Sura: Suratul Mumtahana

Aya : 12

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّبِيُّ إِذَا جَآءَكَ ٱلۡمُؤۡمِنَٰتُ يُبَايِعۡنَكَ عَلَىٰٓ أَن لَّا يُشۡرِكۡنَ بِٱللَّهِ شَيۡـٔٗا وَلَا يَسۡرِقۡنَ وَلَا يَزۡنِينَ وَلَا يَقۡتُلۡنَ أَوۡلَٰدَهُنَّ وَلَا يَأۡتِينَ بِبُهۡتَٰنٖ يَفۡتَرِينَهُۥ بَيۡنَ أَيۡدِيهِنَّ وَأَرۡجُلِهِنَّ وَلَا يَعۡصِينَكَ فِي مَعۡرُوفٖ فَبَايِعۡهُنَّ وَٱسۡتَغۡفِرۡ لَهُنَّ ٱللَّهَۚ إِنَّ ٱللَّهَ غَفُورٞ رَّحِيمٞ

Ya kai wannan Annabi, idan muminai mata suka zo maka suna yi maka mubaya’a a kan ba za su yi shirka da Allah ba, kuma ba za su yi sata ba, ba kuma za su yi zina ba, kuma ba za su kashe ‘ya’yansu ba, kuma ba za su zo da wani qage ba wanda za su qirqira (game da xan da suka haifa) a tsakanin hannayensu da qafafuwansu[1], kuma ba za su sava maka ba game da wani aiki na kirki, to sai ka yi musu mubaya’a, ka kuma nema musu gafarar Allah. Lalle Allah Mai gafara ne, Mai jin qai


1- Kamar yadda suke yi a jahiliyya idan mace ta yi zina da mazaje da yawa sai ta zavi xaya ta danganta masa xan da ta haifa.


Sura: Suratut Taghabun

Aya : 12

وَأَطِيعُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُواْ ٱلرَّسُولَۚ فَإِن تَوَلَّيۡتُمۡ فَإِنَّمَا عَلَىٰ رَسُولِنَا ٱلۡبَلَٰغُ ٱلۡمُبِينُ

Ku bi Allah kuma ku bi Manzon. To idan kuka ba da baya to abin da yake kan Manzonmu kawai shi ne isar da aike



Sura: Suratut Tahrim

Aya : 9

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّبِيُّ جَٰهِدِ ٱلۡكُفَّارَ وَٱلۡمُنَٰفِقِينَ وَٱغۡلُظۡ عَلَيۡهِمۡۚ وَمَأۡوَىٰهُمۡ جَهَنَّمُۖ وَبِئۡسَ ٱلۡمَصِيرُ

Ya kai wannan Annabi, ka yaqi kafirai da munafukai, ka kuma tsananta musu. Makomarsu kuma Jahannama ce; makoma kuwa ta munana



Sura: Suratul Jinn

Aya : 23

إِلَّا بَلَٰغٗا مِّنَ ٱللَّهِ وَرِسَٰلَٰتِهِۦۚ وَمَن يَعۡصِ ٱللَّهَ وَرَسُولَهُۥ فَإِنَّ لَهُۥ نَارَ جَهَنَّمَ خَٰلِدِينَ فِيهَآ أَبَدًا

“Sai dai isar da aike daga Allah da kuma saqwanninsa. Duk kuwa waxanda suka sava wa Allah da Manzonsa, to lalle suna da wutar Jahannama, suna madawwama a cikinta har abada.”



Sura: Suratul Muzzammil

Aya : 1

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلۡمُزَّمِّلُ

Ya kai wannan mai lulluva[1]!


1- Shi ne Manzon Allah () bayan an saukar masa da wahayin farko a kogon Hira, ya dawo gida a tsorace ya lulluva da tufafinsa.


Sura: Suratul Muzzammil

Aya : 2

قُمِ ٱلَّيۡلَ إِلَّا قَلِيلٗا

Ka yi tsaiwar dare sai xan kaxan (daga cikinsa)



Sura: Suratul Muzzammil

Aya : 3

نِّصۡفَهُۥٓ أَوِ ٱنقُصۡ مِنۡهُ قَلِيلًا

Rabinsa ko kuma ka rage kaxan daga gare shi



Sura: Suratul Muzzammil

Aya : 4

أَوۡ زِدۡ عَلَيۡهِ وَرَتِّلِ ٱلۡقُرۡءَانَ تَرۡتِيلًا

Ko ka qara a kansa, ka kuma karanta Alqur’ani daki-daki



Sura: Suratul Muzzammil

Aya : 7

إِنَّ لَكَ فِي ٱلنَّهَارِ سَبۡحٗا طَوِيلٗا

Lalle da rana kana da harkoki masu yawa



Sura: Suratul Muzzammil

Aya : 8

وَٱذۡكُرِ ٱسۡمَ رَبِّكَ وَتَبَتَّلۡ إِلَيۡهِ تَبۡتِيلٗا

Ka kuma ambaci sunan Ubangijinka kuma ka yanke alaqarka da komai don bautarsa



Sura: Suratul Muzzammil

Aya : 10

وَٱصۡبِرۡ عَلَىٰ مَا يَقُولُونَ وَٱهۡجُرۡهُمۡ هَجۡرٗا جَمِيلٗا

Kuma ka yi haquri a kan abin da suke faxa, kuma ka qaurace musu kyakkyawar qauracewa[1]


1- Watau qauracewar da babu cutarwa a cikinta.


Sura: Suratul Muddassir

Aya : 1

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلۡمُدَّثِّرُ

Ya kai mai lulluva[1]


1- Shi ne Annabi () wanda ya lulluva da tufafinsa don tsoron mala’ikan da ya yi idon huxu da shi a karon farko a kogon Hira.


Sura: Suratul Muddassir

Aya : 2

قُمۡ فَأَنذِرۡ

Tashi ka yi gargaxi



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 3

وَرَبَّكَ فَكَبِّرۡ

Kuma ka girmama Ubangijinka



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 4

وَثِيَابَكَ فَطَهِّرۡ

Ka kuma tsarkake tufafinka



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 5

وَٱلرُّجۡزَ فَٱهۡجُرۡ

Ka kuma qaurace wa (bautar) gumaka



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 6

وَلَا تَمۡنُن تَسۡتَكۡثِرُ

Kada kuma ka goranta wa (Ubangijinka) da ganin yawan (ayyukanka na qwarai)[1]


1- Watau kada yawansu ya ruxe shi har ya yi rauni wajen tsayuwa da ayyukan da’awa.


Sura: Suratul Muddassir

Aya : 7

وَلِرَبِّكَ فَٱصۡبِرۡ

Ka kuma yi haquri game da Ubangijinka



Sura: Suratul Qiyama

Aya : 16

لَا تُحَرِّكۡ بِهِۦ لِسَانَكَ لِتَعۡجَلَ بِهِۦٓ

(Allah ya ce da Annabinsa): Kada ka motsa harshenka da shi (Alqur’ani) don gaggauta (karanta) shi



Sura: Suratul Qiyama

Aya : 17

إِنَّ عَلَيۡنَا جَمۡعَهُۥ وَقُرۡءَانَهُۥ

Lalle tattara shi (a zuciyarka) da karanta shi yana kanmu



Sura: Suratul Qiyama

Aya : 18

فَإِذَا قَرَأۡنَٰهُ فَٱتَّبِعۡ قُرۡءَانَهُۥ

Saboda haka idan Muka karanta (maka) shi sai ka bi karatunsa



Sura: Suratul Qiyama

Aya : 19

ثُمَّ إِنَّ عَلَيۡنَا بَيَانَهُۥ

Sannan kuma bayaninsa yana kanmu



Sura: Suratul Insan

Aya : 24

فَٱصۡبِرۡ لِحُكۡمِ رَبِّكَ وَلَا تُطِعۡ مِنۡهُمۡ ءَاثِمًا أَوۡ كَفُورٗا

Saboda haka ka yi haquri da hukuncin Ubangijinka kada kuwa ka bi mai yawan savo ko mai yawan kafircewa daga cikinsu



Sura: Suratul Insan

Aya : 25

وَٱذۡكُرِ ٱسۡمَ رَبِّكَ بُكۡرَةٗ وَأَصِيلٗا

Ka kuma ambaci sunan Ubangijinka safe da yamma



Sura: Suratul Insan

Aya : 26

وَمِنَ ٱلَّيۡلِ فَٱسۡجُدۡ لَهُۥ وَسَبِّحۡهُ لَيۡلٗا طَوِيلًا

Da daddare kuma sai ka yi sujjada a gare Shi, ka kuma yi nafiloli saboda Shi a tsawon dare



Sura: Suratul A’ala

Aya : 9

فَذَكِّرۡ إِن نَّفَعَتِ ٱلذِّكۡرَىٰ

To ka yi wa’azi idan wa’azin zai yi amfani