Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 115

إِنۡ أَنَا۠ إِلَّا نَذِيرٞ مُّبِينٞ

“Ni kawai mai gargaxi ne mai bayyanawa.”



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 116

قَالُواْ لَئِن لَّمۡ تَنتَهِ يَٰنُوحُ لَتَكُونَنَّ مِنَ ٱلۡمَرۡجُومِينَ

Suka ce: “Ya Nuhu, mun rantse idan ba ka daina (faxar abin da kake faxa) ba, tabbas za ka zamanto daga cikin jefaffu!”



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 117

قَالَ رَبِّ إِنَّ قَوۡمِي كَذَّبُونِ

Ya ce: “Ya Ubangijina, lalle mutanena sun qaryata ni



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 118

فَٱفۡتَحۡ بَيۡنِي وَبَيۡنَهُمۡ فَتۡحٗا وَنَجِّنِي وَمَن مَّعِيَ مِنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ

“Ka yi hukunci tsakanina da su, kuma Ka tserar da ni tare da muminan da suke tare da ni.”



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 119

فَأَنجَيۡنَٰهُ وَمَن مَّعَهُۥ فِي ٱلۡفُلۡكِ ٱلۡمَشۡحُونِ

Sai Muka tserar da shi da waxanda suke tare da shi a cikin jirgin ruwan da ke maqare (da mutane da dabbobi)



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 120

ثُمَّ أَغۡرَقۡنَا بَعۡدُ ٱلۡبَاقِينَ

Sannan bayan haka Muka nutsar da sauran



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 121

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ

Lalle a game da wannan tabbas akwai aya; kuma yawancinsu ba su zamanto muminai ba



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 122

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

Kuma lalle Ubangijinka tabbas Shi ne Mabuwayi, Mai jin qai



Sura: Suratul Ankabut

Aya : 14

وَلَقَدۡ أَرۡسَلۡنَا نُوحًا إِلَىٰ قَوۡمِهِۦ فَلَبِثَ فِيهِمۡ أَلۡفَ سَنَةٍ إِلَّا خَمۡسِينَ عَامٗا فَأَخَذَهُمُ ٱلطُّوفَانُ وَهُمۡ ظَٰلِمُونَ

Kuma haqiqa Mun aiko Nuhu zuwa ga mutanensa, sai ya zauna cikinsu shekara dubu ba hamsin, sai (ruwan) Xufana ya ci su, alhalin suna azzalumai



Sura: Suratul Ankabut

Aya : 15

فَأَنجَيۡنَٰهُ وَأَصۡحَٰبَ ٱلسَّفِينَةِ وَجَعَلۡنَٰهَآ ءَايَةٗ لِّلۡعَٰلَمِينَ

Sai Muka tserar da shi tare da mutanen jirgin ruwa, Muka kuma sanya shi (jirgin) aya ga talikai



Sura: Suratul Ahzab

Aya : 7

وَإِذۡ أَخَذۡنَا مِنَ ٱلنَّبِيِّـۧنَ مِيثَٰقَهُمۡ وَمِنكَ وَمِن نُّوحٖ وَإِبۡرَٰهِيمَ وَمُوسَىٰ وَعِيسَى ٱبۡنِ مَرۡيَمَۖ وَأَخَذۡنَا مِنۡهُم مِّيثَٰقًا غَلِيظٗا

Kuma (ka tuna) lokacin da Muka riqi alqawura daga annabawa (na isar da aike), kuma daga gare ka, kuma daga Nuhu da Ibrahimu da Musa da Isa xan Maryamu; Muka kuma riqi alqawari mai kauri daga gare su



Sura: Suratus Saffat

Aya : 75

وَلَقَدۡ نَادَىٰنَا نُوحٞ فَلَنِعۡمَ ٱلۡمُجِيبُونَ

Kuma haqiqa Nuhu ya roqe Mu, to madalla da Masu amsawa



Sura: Suratus Saffat

Aya : 76

وَنَجَّيۡنَٰهُ وَأَهۡلَهُۥ مِنَ ٱلۡكَرۡبِ ٱلۡعَظِيمِ

Muka kuma tserar da shi tare da iyalinsa daga baqin ciki mai girma



Sura: Suratus Saffat

Aya : 77

وَجَعَلۡنَا ذُرِّيَّتَهُۥ هُمُ ٱلۡبَاقِينَ

Muka kuma sanya zuriyarsa su ne suka wanzu



Sura: Suratus Saffat

Aya : 78

وَتَرَكۡنَا عَلَيۡهِ فِي ٱلۡأٓخِرِينَ

Muka kuma bar (kyakkyawan yabo) a gare shi ga ‘yan baya



Sura: Suratus Saffat

Aya : 79

سَلَٰمٌ عَلَىٰ نُوحٖ فِي ٱلۡعَٰلَمِينَ

Aminci ya tabbata ga Nuhu a cikin talikai



Sura: Suratus Saffat

Aya : 80

إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجۡزِي ٱلۡمُحۡسِنِينَ

Lalle Mu kamar haka Muke saka wa masu kyautatawa



Sura: Suratus Saffat

Aya : 81

إِنَّهُۥ مِنۡ عِبَادِنَا ٱلۡمُؤۡمِنِينَ

Lalle shi yana daga bayinmu muminai



Sura: Suratus Saffat

Aya : 82

ثُمَّ أَغۡرَقۡنَا ٱلۡأٓخَرِينَ

Sannan Muka nutsar da sauran



Sura: Suratus Shura

Aya : 13

۞شَرَعَ لَكُم مِّنَ ٱلدِّينِ مَا وَصَّىٰ بِهِۦ نُوحٗا وَٱلَّذِيٓ أَوۡحَيۡنَآ إِلَيۡكَ وَمَا وَصَّيۡنَا بِهِۦٓ إِبۡرَٰهِيمَ وَمُوسَىٰ وَعِيسَىٰٓۖ أَنۡ أَقِيمُواْ ٱلدِّينَ وَلَا تَتَفَرَّقُواْ فِيهِۚ كَبُرَ عَلَى ٱلۡمُشۡرِكِينَ مَا تَدۡعُوهُمۡ إِلَيۡهِۚ ٱللَّهُ يَجۡتَبِيٓ إِلَيۡهِ مَن يَشَآءُ وَيَهۡدِيٓ إِلَيۡهِ مَن يُنِيبُ

Ya shar’anta muku (irin) abin da Ya yi wa Nuhu wahayi da shi na addini, da kuma wanda Muka yiwo maka wahayinsa, da kuma abin da Muka yi wa Ibrahimu da Musa da Isa wasiyya da shi cewa: “Ku tsayar da addini, kuma kada ku rarraba a cikinsa.” Abin da kake kiran kafirai zuwa gare shi ya yi musu nauyi. Allah Yana zavar wanda Ya ga dama zuwa gare shi (addini) Yana kuma shiryar da wanda Ya mayar da al’amarinsa zuwa gare Shi



Sura: Suratul Qamar

Aya : 9

۞كَذَّبَتۡ قَبۡلَهُمۡ قَوۡمُ نُوحٖ فَكَذَّبُواْ عَبۡدَنَا وَقَالُواْ مَجۡنُونٞ وَٱزۡدُجِرَ

Mutanen Nuhu sun qaryata kafin su (Quraishawa), sai suka qaryata Bawanmu suka kuma ce, mahaukaci ne, aka kuma kyare (shi)



Sura: Suratul Qamar

Aya : 10

فَدَعَا رَبَّهُۥٓ أَنِّي مَغۡلُوبٞ فَٱنتَصِرۡ

Sai ya roqi Ubangijinsa (cewa): “Lalle an fi qarfina, sai Ka taimaka.”



Sura: Suratul Qamar

Aya : 11

فَفَتَحۡنَآ أَبۡوَٰبَ ٱلسَّمَآءِ بِمَآءٖ مُّنۡهَمِرٖ

Sai Muka buxe qofofin sama da ruwa mai kwararowa



Sura: Suratul Qamar

Aya : 12

وَفَجَّرۡنَا ٱلۡأَرۡضَ عُيُونٗا فَٱلۡتَقَى ٱلۡمَآءُ عَلَىٰٓ أَمۡرٖ قَدۡ قُدِرَ

Muka kuma vuvvugar da idanuwan ruwa daga qasa, sai ruwayen suka haxu a bisa al’amarin da aka riga aka qaddara



Sura: Suratul Qamar

Aya : 13

وَحَمَلۡنَٰهُ عَلَىٰ ذَاتِ أَلۡوَٰحٖ وَدُسُرٖ

Muka kuma xauke shi a kan (jirgin ruwa) mai alluna da qusoshi



Sura: Suratul Qamar

Aya : 14

تَجۡرِي بِأَعۡيُنِنَا جَزَآءٗ لِّمَن كَانَ كُفِرَ

Yana gudu a kan idonmu, don ya zama sakayya ga wanda aka kafirce wa (watau Nuhu)



Sura: Suratul Qamar

Aya : 15

وَلَقَد تَّرَكۡنَٰهَآ ءَايَةٗ فَهَلۡ مِن مُّدَّكِرٖ

Haqiqa kuma Mun bar (abin da ya faru) ya zama aya, to ko akwai mai wa’azantuwa?



Sura: Suratul Hadid

Aya : 26

وَلَقَدۡ أَرۡسَلۡنَا نُوحٗا وَإِبۡرَٰهِيمَ وَجَعَلۡنَا فِي ذُرِّيَّتِهِمَا ٱلنُّبُوَّةَ وَٱلۡكِتَٰبَۖ فَمِنۡهُم مُّهۡتَدٖۖ وَكَثِيرٞ مِّنۡهُمۡ فَٰسِقُونَ

Haqiqa kuma Mun aiko Nuhu da Ibrahimu, Muka kuma sanya annabta da littafi cikin zuriyarsu; To daga cikinsu akwai shiryayyu, masu yawa kuwa daga cikinsu fasiqai ne



Sura: Suratu Nuh

Aya : 1

إِنَّآ أَرۡسَلۡنَا نُوحًا إِلَىٰ قَوۡمِهِۦٓ أَنۡ أَنذِرۡ قَوۡمَكَ مِن قَبۡلِ أَن يَأۡتِيَهُمۡ عَذَابٌ أَلِيمٞ

Lalle Mu Mun aika Nuhu zuwa ga mutanensa cewa: “Ka gargaxi mutanenka tun kafin azaba mai raxaxi ta zo musu.”



Sura: Suratu Nuh

Aya : 2

قَالَ يَٰقَوۡمِ إِنِّي لَكُمۡ نَذِيرٞ مُّبِينٌ

Ya ce: “Ya ku mutanena, lalle ni mai gargaxi ne mabayyani a gare ku