Sura: Suratus Saffat

Aya : 46

بَيۡضَآءَ لَذَّةٖ لِّلشَّـٰرِبِينَ

Fara fat, ga kuma daxi ga masu sha



Sura: Suratus Saffat

Aya : 47

لَا فِيهَا غَوۡلٞ وَلَا هُمۡ عَنۡهَا يُنزَفُونَ

Babu sa ciwon kai a gare ta, kuma ba za a bugar da su da ita ba



Sura: Suratus Saffat

Aya : 48

وَعِندَهُمۡ قَٰصِرَٰتُ ٱلطَّرۡفِ عِينٞ

A wurinsu kuma akwai mataye masu taqaita kallonsu ga mazajensu, masu qwala-qwalan ido



Sura: Suratus Saffat

Aya : 49

كَأَنَّهُنَّ بَيۡضٞ مَّكۡنُونٞ

Kai ka ce su wani qwai ne a cikin kwasfa



Sura: Suratuz Zukhruf 

Aya : 71

يُطَافُ عَلَيۡهِم بِصِحَافٖ مِّن ذَهَبٖ وَأَكۡوَابٖۖ وَفِيهَا مَا تَشۡتَهِيهِ ٱلۡأَنفُسُ وَتَلَذُّ ٱلۡأَعۡيُنُۖ وَأَنتُمۡ فِيهَا خَٰلِدُونَ

Ana zagayawa tsakaninsu da akusa na zinari da kofuna; a cikinta kuma akwai (duk) abin da rayuka suke sha’awa, idanuwa kuma suke jin daxin (ganinsu); ku kuma a cikinta madawwama ne



Sura: Suratuz Zukhruf 

Aya : 72

وَتِلۡكَ ٱلۡجَنَّةُ ٱلَّتِيٓ أُورِثۡتُمُوهَا بِمَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ

Waccan kuma ita ce Aljannar da aka gadar muku ita saboda abin da kuka kasance kuma aikatawa



Sura: Suratuz Zukhruf 

Aya : 73

لَكُمۡ فِيهَا فَٰكِهَةٞ كَثِيرَةٞ مِّنۡهَا تَأۡكُلُونَ

A cikinta kuna da `ya`yan itatuwa na marmari masu yawa, daga gare su kuma za ku riqa ci



Sura: Suratud Dukhan

Aya : 51

إِنَّ ٱلۡمُتَّقِينَ فِي مَقَامٍ أَمِينٖ

Lalle masu taqawa suna cikin wani amintaccen wuri



Sura: Suratud Dukhan

Aya : 52

فِي جَنَّـٰتٖ وَعُيُونٖ

Cikin lambuna da idanuwan ruwa



Sura: Suratud Dukhan

Aya : 53

يَلۡبَسُونَ مِن سُندُسٖ وَإِسۡتَبۡرَقٖ مُّتَقَٰبِلِينَ

Suna saye da tufafi na alharini mai shara-shara da mai kauri suna fuskantar juna



Sura: Suratud Dukhan

Aya : 54

كَذَٰلِكَ وَزَوَّجۡنَٰهُم بِحُورٍ عِينٖ

Kamar haka ne, Muka kuma aura musu (‘yan matan) Hurul-Ini



Sura: Suratud Dukhan

Aya : 55

يَدۡعُونَ فِيهَا بِكُلِّ فَٰكِهَةٍ ءَامِنِينَ

A cikinta (Aljannar) suna kiran a kawo musu duk wani kayan marmari, suna cikin aminci



Sura: Suratu Muhammad

Aya : 15

مَّثَلُ ٱلۡجَنَّةِ ٱلَّتِي وُعِدَ ٱلۡمُتَّقُونَۖ فِيهَآ أَنۡهَٰرٞ مِّن مَّآءٍ غَيۡرِ ءَاسِنٖ وَأَنۡهَٰرٞ مِّن لَّبَنٖ لَّمۡ يَتَغَيَّرۡ طَعۡمُهُۥ وَأَنۡهَٰرٞ مِّنۡ خَمۡرٖ لَّذَّةٖ لِّلشَّـٰرِبِينَ وَأَنۡهَٰرٞ مِّنۡ عَسَلٖ مُّصَفّٗىۖ وَلَهُمۡ فِيهَا مِن كُلِّ ٱلثَّمَرَٰتِ وَمَغۡفِرَةٞ مِّن رَّبِّهِمۡۖ كَمَنۡ هُوَ خَٰلِدٞ فِي ٱلنَّارِ وَسُقُواْ مَآءً حَمِيمٗا فَقَطَّعَ أَمۡعَآءَهُمۡ

Kwatankwacin Aljannar da aka yi wa masu taqawa alqawari da ita shi ne, a cikinta akwai qoramu na ruwa ba gurvatacce ba, da kuma qoramu na nono da xanxanonsa bai canja ba, da qoramu na giya masu daxi ga mashaya, da qoramu na tatacciyar zuma, kuma suna da kowane irin nau’i na ‘ya’yan itace da kuma gafara daga Ubangijinsu. Yanzu (masu waxannan sa yi) daidai da waxanda za su dawwama a cikin wuta a kuma shayar da su ruwa tafasasshe, sai ya yayyanke kayan cikinsu?



Sura: Suratur Rahman

Aya : 46

وَلِمَنۡ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ جَنَّتَانِ

Duk wanda kuwa ya ji tsoron tsayuwa (gaban) Ubangijinsa yana da Aljanna biyu



Sura: Suratur Rahman

Aya : 47

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Sura: Suratur Rahman

Aya : 48

ذَوَاتَآ أَفۡنَانٖ

Ma’abota rassan bishiyoyi



Sura: Suratur Rahman

Aya : 49

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Sura: Suratur Rahman

Aya : 50

فِيهِمَا عَيۡنَانِ تَجۡرِيَانِ

A cikinsu akwai idanuwa (na ruwa) guda biyu masu gudana



Sura: Suratur Rahman

Aya : 51

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Sura: Suratur Rahman

Aya : 52

فِيهِمَا مِن كُلِّ فَٰكِهَةٖ زَوۡجَانِ

A cikinsu akwai (dangi) biyu na kowane abin marmari



Sura: Suratur Rahman

Aya : 53

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Sura: Suratur Rahman

Aya : 54

مُتَّكِـِٔينَ عَلَىٰ فُرُشِۭ بَطَآئِنُهَا مِنۡ إِسۡتَبۡرَقٖۚ وَجَنَى ٱلۡجَنَّتَيۡنِ دَانٖ

Suna kishingixe a kan shimfixu da shafin cikinsu na kakkauran alhariri ne. Kuma ‘ya’yan bishiyoyin Aljannatai biyun kusa suke (da kowa)



Sura: Suratur Rahman

Aya : 55

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Sura: Suratur Rahman

Aya : 56

فِيهِنَّ قَٰصِرَٰتُ ٱلطَّرۡفِ لَمۡ يَطۡمِثۡهُنَّ إِنسٞ قَبۡلَهُمۡ وَلَا جَآنّٞ

A cikinsu akwai (mata) masu taqaita kallo (ga mazajensu, waxanda) wani mutum ko aljan bai tava shafar su ba a gabaninsu



Sura: Suratur Rahman

Aya : 57

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Sura: Suratur Rahman

Aya : 58

كَأَنَّهُنَّ ٱلۡيَاقُوتُ وَٱلۡمَرۡجَانُ

Kai ka ce su yaqutu ne da murjani



Sura: Suratur Rahman

Aya : 59

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Sura: Suratur Rahman

Aya : 60

هَلۡ جَزَآءُ ٱلۡإِحۡسَٰنِ إِلَّا ٱلۡإِحۡسَٰنُ

Shin akwai wani sakamako na kyautatawa in ba kyautatawa ba?



Sura: Suratur Rahman

Aya : 61

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Sura: Suratur Rahman

Aya : 62

وَمِن دُونِهِمَا جَنَّتَانِ

A qasa da su kuma akwai wasu aljannatai guda biyu