Sura: Suratur Rahman

Aya : 63

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Sura: Suratur Rahman

Aya : 64

مُدۡهَآمَّتَانِ

Masu tsananin kore



Sura: Suratur Rahman

Aya : 65

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Sura: Suratur Rahman

Aya : 66

فِيهِمَا عَيۡنَانِ نَضَّاخَتَانِ

A cikinsu (kuma) akwai idanuwan (ruwa) guda biyu masu feshi



Sura: Suratur Rahman

Aya : 67

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Sura: Suratur Rahman

Aya : 68

فِيهِمَا فَٰكِهَةٞ وَنَخۡلٞ وَرُمَّانٞ

A cikinsu (kuma) akwai abin marmari da dabino da ruman



Sura: Suratur Rahman

Aya : 69

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Sura: Suratur Rahman

Aya : 70

فِيهِنَّ خَيۡرَٰتٌ حِسَانٞ

A cikinsu (watau gidajen Aljannar) akwai mata nagartattu kyawawa



Sura: Suratur Rahman

Aya : 71

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Sura: Suratur Rahman

Aya : 72

حُورٞ مَّقۡصُورَٰتٞ فِي ٱلۡخِيَامِ

(Matayen) masu fari da baqin ido ne, suna kawwame cikin tantuna



Sura: Suratur Rahman

Aya : 73

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Sura: Suratur Rahman

Aya : 74

لَمۡ يَطۡمِثۡهُنَّ إِنسٞ قَبۡلَهُمۡ وَلَا جَآنّٞ

Wani mutum ko aljan bai tava shafar su ba a gabaninsu



Sura: Suratur Rahman

Aya : 75

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Sura: Suratur Rahman

Aya : 76

مُتَّكِـِٔينَ عَلَىٰ رَفۡرَفٍ خُضۡرٖ وَعَبۡقَرِيٍّ حِسَانٖ

Suna kishingixe a kan matasan kai koraye, da kuma kilisai kyawawa



Sura: Suratur Rahman

Aya : 77

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 15

عَلَىٰ سُرُرٖ مَّوۡضُونَةٖ

Suna kan gadaje masu adon zinari



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 16

مُّتَّكِـِٔينَ عَلَيۡهَا مُتَقَٰبِلِينَ

Suna kishingixe a kansu suna fuskantar juna



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 17

يَطُوفُ عَلَيۡهِمۡ وِلۡدَٰنٞ مُّخَلَّدُونَ

Yara samari dawwamammu (masu hidima) za su riqa zagaya su



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 18

بِأَكۡوَابٖ وَأَبَارِيقَ وَكَأۡسٖ مِّن مَّعِينٖ

Da kofuna (marasa mariqai) da butoci masu hannaye da kuma qoquna na giya



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 19

لَّا يُصَدَّعُونَ عَنۡهَا وَلَا يُنزِفُونَ

Ba sa ciwon kai saboda ita, kuma ba sa buguwa



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 20

وَفَٰكِهَةٖ مِّمَّا يَتَخَيَّرُونَ

Da kuma ababan marmari na abin da suke so su zava



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 21

وَلَحۡمِ طَيۡرٖ مِّمَّا يَشۡتَهُونَ

Da kuma naman tsuntsaye na abin da suke sha’awa



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 22

وَحُورٌ عِينٞ

Da kuma matan Hurul-Ini



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 23

كَأَمۡثَٰلِ ٱللُّؤۡلُوِٕ ٱلۡمَكۡنُونِ

Kamar misalin lu’ulu’u da yake cikin kwasfa



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 24

جَزَآءَۢ بِمَا كَانُواْ يَعۡمَلُونَ

Sakamako ne na abin da suka kasance suna aikatawa



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 25

لَا يَسۡمَعُونَ فِيهَا لَغۡوٗا وَلَا تَأۡثِيمًا

Ba sa kuma jin wani zancen banza da mai sa zunubi a cikinta



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 26

إِلَّا قِيلٗا سَلَٰمٗا سَلَٰمٗا

Sai dai faxar salamun-salamun[1]


1- Watau sallamar mala’iku a gare su da wadda za su riqa yi wa junansu.


Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 28

فِي سِدۡرٖ مَّخۡضُودٖ

Suna cikin ‘ya’yan itacen magarya marasa qaya



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 29

وَطَلۡحٖ مَّنضُودٖ

Da kuma ayaba mai ‘ya’ya dava-dava



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 30

وَظِلّٖ مَّمۡدُودٖ

Da inuwa madawwamiya