Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 31

وَمَآءٖ مَّسۡكُوبٖ

Da kuma ruwa mai kwarara



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 32

وَفَٰكِهَةٖ كَثِيرَةٖ

Da ababen marmari masu yawa



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 33

لَّا مَقۡطُوعَةٖ وَلَا مَمۡنُوعَةٖ

Ba masu yankewa ba kuma ba ababen hanawa ba



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 34

وَفُرُشٖ مَّرۡفُوعَةٍ

Da shimfixu masu daraja



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 35

إِنَّآ أَنشَأۡنَٰهُنَّ إِنشَآءٗ

Lalle Mu ne Muka qage su (‘yan matan Aljanna) sabuwar qagowa



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 36

فَجَعَلۡنَٰهُنَّ أَبۡكَارًا

Sannan Muka sanya su budurwai



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 37

عُرُبًا أَتۡرَابٗا

Masu begen mazajensu, tsarekun juna



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 38

لِّأَصۡحَٰبِ ٱلۡيَمِينِ

Don ma’abota hannun dama



Sura: Suratul Hadid

Aya : 21

سَابِقُوٓاْ إِلَىٰ مَغۡفِرَةٖ مِّن رَّبِّكُمۡ وَجَنَّةٍ عَرۡضُهَا كَعَرۡضِ ٱلسَّمَآءِ وَٱلۡأَرۡضِ أُعِدَّتۡ لِلَّذِينَ ءَامَنُواْ بِٱللَّهِ وَرُسُلِهِۦۚ ذَٰلِكَ فَضۡلُ ٱللَّهِ يُؤۡتِيهِ مَن يَشَآءُۚ وَٱللَّهُ ذُو ٱلۡفَضۡلِ ٱلۡعَظِيمِ

Ku yi rige-rige zuwa neman gafara daga Ubangijinku da Aljanna wadda faxinta kamar faxin sammai da qasa yake, an tanade ta don waxanda suka yi imani da Allah da manzanninsa. Wannan falalar Allah ce da Yake ba da ita ga wanda Ya ga dama. Allah kuwa Ma’abocin falala ne, Mai girma



Sura: Suratul Haqqa

Aya : 22

فِي جَنَّةٍ عَالِيَةٖ

Cikin Aljanna maxaukakiya



Sura: Suratul Haqqa

Aya : 23

قُطُوفُهَا دَانِيَةٞ

‘Ya’yan itatuwanta dab da dab suke



Sura: Suratul Insan

Aya : 12

وَجَزَىٰهُم بِمَا صَبَرُواْ جَنَّةٗ وَحَرِيرٗا

Ya kuma saka musu da Aljanna da alharini saboda haqurin da suka yi



Sura: Suratul Insan

Aya : 13

مُّتَّكِـِٔينَ فِيهَا عَلَى ٱلۡأَرَآئِكِۖ لَا يَرَوۡنَ فِيهَا شَمۡسٗا وَلَا زَمۡهَرِيرٗا

Suna masu kishingixa a cikinta a kan gadaje; ba sa ganin rana ko jin tsananin sanyi a cikinta



Sura: Suratul Insan

Aya : 14

وَدَانِيَةً عَلَيۡهِمۡ ظِلَٰلُهَا وَذُلِّلَتۡ قُطُوفُهَا تَذۡلِيلٗا

Inuwoyinta kuma suna kusa da su, an kuma hore musu ‘ya’yan itatuwanta matuqar horewa



Sura: Suratul Insan

Aya : 15

وَيُطَافُ عَلَيۡهِم بِـَٔانِيَةٖ مِّن فِضَّةٖ وَأَكۡوَابٖ كَانَتۡ قَوَارِيرَا۠

Ana kuma kai-kawo a tsakaninsu da qorai na azurfa da kofuna waxanda suka kasance na qarau



Sura: Suratul Insan

Aya : 16

قَوَارِيرَاْ مِن فِضَّةٖ قَدَّرُوهَا تَقۡدِيرٗا

Qarau xin na azurfa ne, sun auna su, aunawa daidai da buqata



Sura: Suratul Insan

Aya : 17

وَيُسۡقَوۡنَ فِيهَا كَأۡسٗا كَانَ مِزَاجُهَا زَنجَبِيلًا

Ana kuma shayar da su wata giya a cikinta, wadda mahaxinta ya kasance citta mai yatsu ce



Sura: Suratul Insan

Aya : 18

عَيۡنٗا فِيهَا تُسَمَّىٰ سَلۡسَبِيلٗا

Wani marmaro ne a cikinta da ake kiran sa Salsabilu



Sura: Suratul Insan

Aya : 19

۞وَيَطُوفُ عَلَيۡهِمۡ وِلۡدَٰنٞ مُّخَلَّدُونَ إِذَا رَأَيۡتَهُمۡ حَسِبۡتَهُمۡ لُؤۡلُؤٗا مَّنثُورٗا

Samari hadimai dawwamammu (da ba sa tsufa) kuma suna kai-kawo tsakaninsu, idan ka gan su sai ka yi tsammanin su wani lu’ulu’u ne da aka baza



Sura: Suratul Insan

Aya : 20

وَإِذَا رَأَيۡتَ ثَمَّ رَأَيۡتَ نَعِيمٗا وَمُلۡكٗا كَبِيرًا

Idan kuma ka yi kallo a can, za ka ga ni’ima da kuma mulki qasaitacce



Sura: Suratul Insan

Aya : 21

عَٰلِيَهُمۡ ثِيَابُ سُندُسٍ خُضۡرٞ وَإِسۡتَبۡرَقٞۖ وَحُلُّوٓاْ أَسَاوِرَ مِن فِضَّةٖ وَسَقَىٰهُمۡ رَبُّهُمۡ شَرَابٗا طَهُورًا

Suna sanye da korayen tufafin alharini marar kauri da na alharini mai kauri; aka kuma yi musu ado da warawarai na azurfa, Ubangijinsu kuma Ya shayar da su abin sha mai tsarki



Sura: Suratul Insan

Aya : 22

إِنَّ هَٰذَا كَانَ لَكُمۡ جَزَآءٗ وَكَانَ سَعۡيُكُم مَّشۡكُورًا

Lalle wannan ya kasance sakamako ne a gare ku, kuma aikinku ya kasance abin godewa



Sura: Suratun Naba’i

Aya : 31

إِنَّ لِلۡمُتَّقِينَ مَفَازًا

Lalle masu taqawa suna da babban rabo



Sura: Suratun Naba’i

Aya : 32

حَدَآئِقَ وَأَعۡنَٰبٗا

(Su ne) gonaki da inabai



Sura: Suratun Naba’i

Aya : 33

وَكَوَاعِبَ أَتۡرَابٗا

Da ‘yan mata tsaraiku



Sura: Suratun Naba’i

Aya : 34

وَكَأۡسٗا دِهَاقٗا

Da kofin (giya) cikakke



Sura: Suratun Naba’i

Aya : 35

لَّا يَسۡمَعُونَ فِيهَا لَغۡوٗا وَلَا كِذَّـٰبٗا

Ba sa jin maganar banza a cikinta ko kuma qarya



Sura: Suratun Naba’i

Aya : 36

جَزَآءٗ مِّن رَّبِّكَ عَطَآءً حِسَابٗا

Sakamako ne daga Ubangijinka, kyauta ce a lissafe (gwargwadon aikin kowa)



Sura: Suratul Muxaffifin

Aya : 25

يُسۡقَوۡنَ مِن رَّحِيقٖ مَّخۡتُومٍ

Ana shayar da su giyar da aka rufe (bakin mazubinta)



Sura: Suratul Muxaffifin

Aya : 26

خِتَٰمُهُۥ مِسۡكٞۚ وَفِي ذَٰلِكَ فَلۡيَتَنَافَسِ ٱلۡمُتَنَٰفِسُونَ

(Har) qarshensa (qamshin) almiski ne. To game da wannan kuwa lalle masu gasa su yi gasa