Sura: Suratul Qamar

Aya : 55

فِي مَقۡعَدِ صِدۡقٍ عِندَ مَلِيكٖ مُّقۡتَدِرِۭ

A mazauni na gaskiya a wurin Mai mulki, Mai iko



Sura: Suratur Rahman

Aya : 46

وَلِمَنۡ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ جَنَّتَانِ

Duk wanda kuwa ya ji tsoron tsayuwa (gaban) Ubangijinsa yana da Aljanna biyu



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 10

وَٱلسَّـٰبِقُونَ ٱلسَّـٰبِقُونَ

Da kuma masu rige-rige (zuwa alheri)



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 11

أُوْلَـٰٓئِكَ ٱلۡمُقَرَّبُونَ

Waxannan su ne makusanta



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 12

فِي جَنَّـٰتِ ٱلنَّعِيمِ

A cikin gidajen Aljanna na ni’ima



Sura: Suratul Qalam

Aya : 34

إِنَّ لِلۡمُتَّقِينَ عِندَ رَبِّهِمۡ جَنَّـٰتِ ٱلنَّعِيمِ

Lalle masu taqawa suna da gidajen Aljannar ni’ima a wurin Ubangijinsu



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 23

ٱلَّذِينَ هُمۡ عَلَىٰ صَلَاتِهِمۡ دَآئِمُونَ

Waxanda suke masu dawwama a kan sallarsu



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 24

وَٱلَّذِينَ فِيٓ أَمۡوَٰلِهِمۡ حَقّٞ مَّعۡلُومٞ

Waxanda kuma suke akwai haqqi sananne a cikin dukiyoyinsu



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 25

لِّلسَّآئِلِ وَٱلۡمَحۡرُومِ

Ga mai roqo da wanda ake hana wa (saboda ba ya roqo)



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 26

وَٱلَّذِينَ يُصَدِّقُونَ بِيَوۡمِ ٱلدِّينِ

Waxanda kuma suke gaskata ranar sakamako



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 27

وَٱلَّذِينَ هُم مِّنۡ عَذَابِ رَبِّهِم مُّشۡفِقُونَ

Waxanda kuma suke tsoron azabar Ubangijinsu



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 28

إِنَّ عَذَابَ رَبِّهِمۡ غَيۡرُ مَأۡمُونٖ

Lalle azabar Ubangijinsu ba abar amincewa ba ce



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 29

وَٱلَّذِينَ هُمۡ لِفُرُوجِهِمۡ حَٰفِظُونَ

Waxanda kuma suke kiyaye al’aurarsu (daga yin zina)



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 30

إِلَّا عَلَىٰٓ أَزۡوَٰجِهِمۡ أَوۡ مَا مَلَكَتۡ أَيۡمَٰنُهُمۡ فَإِنَّهُمۡ غَيۡرُ مَلُومِينَ

Sai a wajan matayensu ko kuma qwarqarorinsu; to su a nan ba ababen zargi ba ne



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 31

فَمَنِ ٱبۡتَغَىٰ وَرَآءَ ذَٰلِكَ فَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡعَادُونَ

To duk wanda ya nemi (wani abu) bayan wannan, to waxannan su ne masu qetare iyaka



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 32

وَٱلَّذِينَ هُمۡ لِأَمَٰنَٰتِهِمۡ وَعَهۡدِهِمۡ رَٰعُونَ

Waxanda kuma suke kiyaye amanoninsu da alqawuransu



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 33

وَٱلَّذِينَ هُم بِشَهَٰدَٰتِهِمۡ قَآئِمُونَ

Waxanda kuma suke tsai da shaidarsu



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 34

وَٱلَّذِينَ هُمۡ عَلَىٰ صَلَاتِهِمۡ يُحَافِظُونَ

Waxanda kuma suke kiyaye sallolinsu



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 35

أُوْلَـٰٓئِكَ فِي جَنَّـٰتٖ مُّكۡرَمُونَ

Waxannan su ne waxanda ake girmamawa cikin gidajen Aljanna



Sura: Suratul Mursalat

Aya : 41

إِنَّ ٱلۡمُتَّقِينَ فِي ظِلَٰلٖ وَعُيُونٖ

Lalle masu taqawa suna cikin inuwoyi da idanuwan ruwa



Sura: Suratul Mursalat

Aya : 42

وَفَوَٰكِهَ مِمَّا يَشۡتَهُونَ

Da kuma ababan marmari daga abin da suke sha’awa



Sura: Suratul Mursalat

Aya : 43

كُلُواْ وَٱشۡرَبُواْ هَنِيٓـَٔۢا بِمَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ

Ku ci kuma ku sha kuna masu farin ciki saboda abin da kuka kasance kuna aikatawa



Sura: Suratul Mursalat

Aya : 44

إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجۡزِي ٱلۡمُحۡسِنِينَ

Lalle Mu kamar haka Muke saka wa masu kyautatawa



Sura: Suratun Nazi’at

Aya : 40

وَأَمَّا مَنۡ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ وَنَهَى ٱلنَّفۡسَ عَنِ ٱلۡهَوَىٰ

Duk wanda kuma ya ji tsoron tsayuwa gaban Ubangijinsa, ya kuma hana zuciya bin abin da take so



Sura: Suratun Nazi’at

Aya : 41

فَإِنَّ ٱلۡجَنَّةَ هِيَ ٱلۡمَأۡوَىٰ

To lalle Aljanna ita ce makoma



Sura: Suratul Muxaffifin

Aya : 22

إِنَّ ٱلۡأَبۡرَارَ لَفِي نَعِيمٍ

Lalle masu biyayya tabbas suna cikin ni’ima



Sura: Suratul Muxaffifin

Aya : 23

عَلَى ٱلۡأَرَآئِكِ يَنظُرُونَ

A kan gadaje suna kallo



Sura: Suratul Muxaffifin

Aya : 24

تَعۡرِفُ فِي وُجُوهِهِمۡ نَضۡرَةَ ٱلنَّعِيمِ

Za ka gane hasken ni’ima a fuskokinsu[1]


1- Watau fuskokinsu suna sheqi da annuri.


Sura: Suratul Buruj

Aya : 11

إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ لَهُمۡ جَنَّـٰتٞ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُۚ ذَٰلِكَ ٱلۡفَوۡزُ ٱلۡكَبِيرُ

Lalle waxanda suka yi imani suka kuma yi ayyuka nagari suna da gidajen Aljanna waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu. Wannan kuwa shi ne babban rabo



Sura: Suratul Fajr

Aya : 27

يَـٰٓأَيَّتُهَا ٱلنَّفۡسُ ٱلۡمُطۡمَئِنَّةُ

(Za a ce): Ya kai wannan rai mai nutsuwa