Sura: Suratul Qamar

Aya : 55

فِي مَقۡعَدِ صِدۡقٍ عِندَ مَلِيكٖ مُّقۡتَدِرِۭ

A mazauni na gaskiya a wurin Mai mulki, Mai iko



Sura: Suratul Insan

Aya : 5

إِنَّ ٱلۡأَبۡرَارَ يَشۡرَبُونَ مِن كَأۡسٖ كَانَ مِزَاجُهَا كَافُورًا

Lalle mutane nagari suna sha daga wani kofin (giya) da mahaxinta ya kasance kafur ne[1]


1- Watau mai daxin qamshi.


Sura: Suratul Insan

Aya : 6

عَيۡنٗا يَشۡرَبُ بِهَا عِبَادُ ٱللَّهِ يُفَجِّرُونَهَا تَفۡجِيرٗا

Wani marmaro ne da bayin Allah suke sha daga gare shi suna vuvvugo shi vuvvugowa ta haqiqa



Sura: Suratul Insan

Aya : 7

يُوفُونَ بِٱلنَّذۡرِ وَيَخَافُونَ يَوۡمٗا كَانَ شَرُّهُۥ مُسۡتَطِيرٗا

Suna cika alqawari na bakance suna kuma tsoron ranar da sharrinta ya kasance mai bazuwa ne



Sura: Suratul Insan

Aya : 8

وَيُطۡعِمُونَ ٱلطَّعَامَ عَلَىٰ حُبِّهِۦ مِسۡكِينٗا وَيَتِيمٗا وَأَسِيرًا

Suna kuma ciyar da abinci tare da suna son sa ga miskini da maraya da kuma ribataccen yaqi



Sura: Suratul Insan

Aya : 9

إِنَّمَا نُطۡعِمُكُمۡ لِوَجۡهِ ٱللَّهِ لَا نُرِيدُ مِنكُمۡ جَزَآءٗ وَلَا شُكُورًا

(Suna cewa): “Mu kawai muna ciyar da ku ne saboda Allah, ba ma nufin sakamako ko godiya daga wurinka



Sura: Suratul Insan

Aya : 10

إِنَّا نَخَافُ مِن رَّبِّنَا يَوۡمًا عَبُوسٗا قَمۡطَرِيرٗا

“Lalle mu muna jin tsoron rana mai sa xaure fuska, matsananciya daga Ubangijinmu



Sura: Suratul Insan

Aya : 11

فَوَقَىٰهُمُ ٱللَّهُ شَرَّ ذَٰلِكَ ٱلۡيَوۡمِ وَلَقَّىٰهُمۡ نَضۡرَةٗ وَسُرُورٗا

Sai Allah Ya kare su (daga) sharrin wannan ranar Ya kuma ba su haske (a fuskokinsu) da kuma farin ciki



Sura: Suratul Insan

Aya : 12

وَجَزَىٰهُم بِمَا صَبَرُواْ جَنَّةٗ وَحَرِيرٗا

Ya kuma saka musu da Aljanna da alharini saboda haqurin da suka yi



Sura: Suratul Infixar

Aya : 13

إِنَّ ٱلۡأَبۡرَارَ لَفِي نَعِيمٖ

Lalle mutanen kirki tabbas suna cikin ni’ima



Sura: Suratul Fajr

Aya : 27

يَـٰٓأَيَّتُهَا ٱلنَّفۡسُ ٱلۡمُطۡمَئِنَّةُ

(Za a ce): Ya kai wannan rai mai nutsuwa



Sura: Suratul Fajr

Aya : 28

ٱرۡجِعِيٓ إِلَىٰ رَبِّكِ رَاضِيَةٗ مَّرۡضِيَّةٗ

Ka koma zuwa ga Ubangijinka kana mai yarda (da sakamako), abin yarda



Sura: Suratul Fajr

Aya : 29

فَٱدۡخُلِي فِي عِبَٰدِي

Don haka ka shiga cikin bayina



Sura: Suratul Fajr

Aya : 30

وَٱدۡخُلِي جَنَّتِي

Ka kuma shiga Aljannata