Sura: Suratuz Zariyat

Aya : 44

فَعَتَوۡاْ عَنۡ أَمۡرِ رَبِّهِمۡ فَأَخَذَتۡهُمُ ٱلصَّـٰعِقَةُ وَهُمۡ يَنظُرُونَ

Sai suka yi tsaurin kai game da umarnin Ubangijinsu, saboda haka tsawa ta faxa musu alhali kuwa suna kallo



Sura: Suratuz Zariyat

Aya : 45

فَمَا ٱسۡتَطَٰعُواْ مِن قِيَامٖ وَمَا كَانُواْ مُنتَصِرِينَ

To ba su sami damar tsayuwa ba, kuma ba su zamanto masu taimaka wa (junansu) ba



Sura: Suratun Najm

Aya : 51

وَثَمُودَاْ فَمَآ أَبۡقَىٰ

“Da kuma Samudawa, don haka bai bar saura ba



Sura: Suratul Qamar

Aya : 23

كَذَّبَتۡ ثَمُودُ بِٱلنُّذُرِ

Samudawa sun qaryata gargaxi



Sura: Suratul Qamar

Aya : 24

فَقَالُوٓاْ أَبَشَرٗا مِّنَّا وَٰحِدٗا نَّتَّبِعُهُۥٓ إِنَّآ إِذٗا لَّفِي ضَلَٰلٖ وَسُعُرٍ

Sannan suka ce: “Yanzu mutum xaya daga cikinmu ne za mu bi? To lalle idan mun yi haka, mun tabbata cikin vata da hauka



Sura: Suratul Qamar

Aya : 25

أَءُلۡقِيَ ٱلذِّكۡرُ عَلَيۡهِ مِنۢ بَيۡنِنَا بَلۡ هُوَ كَذَّابٌ أَشِرٞ

“Yanzu (zai yiwu) a saukar masa da wahayi a tsakaninmu? A’a, shi dai maqaryaci ne mai tsananin girman kai.”



Sura: Suratul Qamar

Aya : 26

سَيَعۡلَمُونَ غَدٗا مَّنِ ٱلۡكَذَّابُ ٱلۡأَشِرُ

A gobe lalle za su san wane ne maqaryacin mai girman kai



Sura: Suratul Qamar

Aya : 27

إِنَّا مُرۡسِلُواْ ٱلنَّاقَةِ فِتۡنَةٗ لَّهُمۡ فَٱرۡتَقِبۡهُمۡ وَٱصۡطَبِرۡ

Lalle Mu Masu aiko taguwa ne don ta zama fitina a gare su, saboda haka ka saurara musu, kuma ka jure



Sura: Suratul Qamar

Aya : 28

وَنَبِّئۡهُمۡ أَنَّ ٱلۡمَآءَ قِسۡمَةُۢ بَيۡنَهُمۡۖ كُلُّ شِرۡبٖ مُّحۡتَضَرٞ

Kuma ka ba su labarin cewa ruwan sha an raba ne tsakaninsu (da ita taguwar); kowane akwai ranar shansa



Sura: Suratul Qamar

Aya : 29

فَنَادَوۡاْ صَاحِبَهُمۡ فَتَعَاطَىٰ فَعَقَرَ

Sai suka kirawo (shaqiyin) abokin nasu sai ya xauki (abin sara) sai ya sare ta



Sura: Suratul Qamar

Aya : 30

فَكَيۡفَ كَانَ عَذَابِي وَنُذُرِ

To qaqa azabata da gargaxina suka kasance?



Sura: Suratul Qamar

Aya : 31

إِنَّآ أَرۡسَلۡنَا عَلَيۡهِمۡ صَيۡحَةٗ وَٰحِدَةٗ فَكَانُواْ كَهَشِيمِ ٱلۡمُحۡتَظِرِ

Lalle Mun aika musu da tsawa guda xaya, sai suka zamo kamar duddugar ciyawa a garken makiyayi



Sura: Suratul Haqqa

Aya : 4

كَذَّبَتۡ ثَمُودُ وَعَادُۢ بِٱلۡقَارِعَةِ

Samudawa da Adawa sun qaryata mai qwanqwasa (zukata da tsoro)



Sura: Suratul Haqqa

Aya : 5

فَأَمَّا ثَمُودُ فَأُهۡلِكُواْ بِٱلطَّاغِيَةِ

To amma Samudawa sai aka halaka su da tsawa mai tsanani



Sura: Suratul Haqqa

Aya : 6

وَأَمَّا عَادٞ فَأُهۡلِكُواْ بِرِيحٖ صَرۡصَرٍ عَاتِيَةٖ

Adawa kuma sai aka hallaka su da iska mai tsananin sanyi mai qarfi



Sura: Suratul Haqqa

Aya : 7

سَخَّرَهَا عَلَيۡهِمۡ سَبۡعَ لَيَالٖ وَثَمَٰنِيَةَ أَيَّامٍ حُسُومٗاۖ فَتَرَى ٱلۡقَوۡمَ فِيهَا صَرۡعَىٰ كَأَنَّهُمۡ أَعۡجَازُ نَخۡلٍ خَاوِيَةٖ

Ya aiko musu da ita dare bakwai da wuni takwas a jere, sai ka riqa ganin mutane a cikinta matattu a yashe, kai ka ce rarakakkun kututturan dabinai ne (a zube)



Sura: Suratul Haqqa

Aya : 8

فَهَلۡ تَرَىٰ لَهُم مِّنۢ بَاقِيَةٖ

To shin za ka iya ganin sauran vurvushinsu?



Sura: Suratul Fajr

Aya : 9

وَثَمُودَ ٱلَّذِينَ جَابُواْ ٱلصَّخۡرَ بِٱلۡوَادِ

Da kuma Samudawa waxanda suka fafe duwatsu a wurin da ake kira Wadil-Qura



Sura: Suratus Shams

Aya : 11

كَذَّبَتۡ ثَمُودُ بِطَغۡوَىٰهَآ

Samudawa sun qaryata saboda xagawarsu



Sura: Suratus Shams

Aya : 12

إِذِ ٱنۢبَعَثَ أَشۡقَىٰهَا

Yayin da mafi tsagerancinsu ya zabura



Sura: Suratus Shams

Aya : 13

فَقَالَ لَهُمۡ رَسُولُ ٱللَّهِ نَاقَةَ ٱللَّهِ وَسُقۡيَٰهَا

Sai Manzon Allah[1] ya ce da su: “Ku bar taguwar Allah da (ranar) shanta.”


1- Watau Annabi Salihu ().


Sura: Suratus Shams

Aya : 14

فَكَذَّبُوهُ فَعَقَرُوهَا فَدَمۡدَمَ عَلَيۡهِمۡ رَبُّهُم بِذَنۢبِهِمۡ فَسَوَّىٰهَا

Sai suka qaryata shi sannan suka soke ta, sai Ubangijinsu Ya kama su da azaba saboda zunubinsu, sai Ya daidaita ta (watau qabilar wajen azaba)



Sura: Suratus Shams

Aya : 15

وَلَا يَخَافُ عُقۡبَٰهَا

Kuma ba Ya tsoron abin da zai biyo bayanta[1]


1- Watau ba ya jin tsoron wani abu da hallaka su za ta haifar nan gaba.