Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 24

وَٱلَّذِينَ فِيٓ أَمۡوَٰلِهِمۡ حَقّٞ مَّعۡلُومٞ

Waxanda kuma suke akwai haqqi sananne a cikin dukiyoyinsu



Sura: Suratul Fajr

Aya : 20

وَتُحِبُّونَ ٱلۡمَالَ حُبّٗا جَمّٗا

Kuma kuna son dukiya so mai yawa



Sura: Suratul Balad

Aya : 6

يَقُولُ أَهۡلَكۡتُ مَالٗا لُّبَدًا

Yana cewa: “Na vatar da dukiya mai ximbin yawa.”



Sura: Suratul Balad

Aya : 7

أَيَحۡسَبُ أَن لَّمۡ يَرَهُۥٓ أَحَدٌ

Shin yana tsammanin cewa ba wanda ya gan shi?



Sura: Suratul Lail

Aya : 8

وَأَمَّا مَنۢ بَخِلَ وَٱسۡتَغۡنَىٰ

Amma kuma wanda ya yi rowa (da haqqin Allah) ya kuma wadatu (da neman lada)



Sura: Suratul Lail

Aya : 9

وَكَذَّبَ بِٱلۡحُسۡنَىٰ

Kuma ya qaryata (sakamako) mafi kyau



Sura: Suratul Lail

Aya : 10

فَسَنُيَسِّرُهُۥ لِلۡعُسۡرَىٰ

To lalle ne za Mu hore masa (hanyar) wuta



Sura: Suratul Lail

Aya : 11

وَمَا يُغۡنِي عَنۡهُ مَالُهُۥٓ إِذَا تَرَدَّىٰٓ

Dukiyarsa kuma ba za ta amfane shi ba idan ya gangara (cikin wuta)



Sura: Suratul Lail

Aya : 18

ٱلَّذِي يُؤۡتِي مَالَهُۥ يَتَزَكَّىٰ

Wanda yake ba da dukiyarsa yana neman tsarkaka



Sura: Suratul Humaza

Aya : 2

ٱلَّذِي جَمَعَ مَالٗا وَعَدَّدَهُۥ

Wanda ya tara dukiya ya qididdige ta



Sura: Suratul Humaza

Aya : 3

يَحۡسَبُ أَنَّ مَالَهُۥٓ أَخۡلَدَهُۥ

Yana zaton cewa dukiyarsa za ta dawwamar da shi



Sura: Suratul Masad

Aya : 2

مَآ أَغۡنَىٰ عَنۡهُ مَالُهُۥ وَمَا كَسَبَ

Dukiyarsa da abin da ya tsuwurwurta ba su amfana masa komai ba