Sura: Suratul Insan

Aya : 25

وَٱذۡكُرِ ٱسۡمَ رَبِّكَ بُكۡرَةٗ وَأَصِيلٗا

Ka kuma ambaci sunan Ubangijinka safe da yamma



Sura: Suratul Insan

Aya : 26

وَمِنَ ٱلَّيۡلِ فَٱسۡجُدۡ لَهُۥ وَسَبِّحۡهُ لَيۡلٗا طَوِيلًا

Da daddare kuma sai ka yi sujjada a gare Shi, ka kuma yi nafiloli saboda Shi a tsawon dare



Sura: Suratul Bayyina

Aya : 5

وَمَآ أُمِرُوٓاْ إِلَّا لِيَعۡبُدُواْ ٱللَّهَ مُخۡلِصِينَ لَهُ ٱلدِّينَ حُنَفَآءَ وَيُقِيمُواْ ٱلصَّلَوٰةَ وَيُؤۡتُواْ ٱلزَّكَوٰةَۚ وَذَٰلِكَ دِينُ ٱلۡقَيِّمَةِ

Ba a kuma umarce su ba sai don su bauta wa Allah suna masu tsantsanta addini gare Shi, suna masu kauce wa varna, suna kuma tsayar da salla, kuma suna ba da zakka. Wannan kuwa shi ne addinin miqaqqiyar hanya



Sura: Suratu Quraish

Aya : 3

فَلۡيَعۡبُدُواْ رَبَّ هَٰذَا ٱلۡبَيۡتِ

To sai su bauta wa Ubangijin wannan Xakin[1]


1- Watau Xakin Ka’aba mai alfarma.


Sura: Suratu Quraish

Aya : 4

ٱلَّذِيٓ أَطۡعَمَهُم مِّن جُوعٖ وَءَامَنَهُم مِّنۡ خَوۡفِۭ

Wanda Ya ciyar da su daga yunwa, Ya kuma amintar da su daga tsoro



Sura: Suratul Kafirun

Aya : 1

قُلۡ يَـٰٓأَيُّهَا ٱلۡكَٰفِرُونَ

Ka ce: “Ya ku waxannan kafirai



Sura: Suratul Kafirun

Aya : 2

لَآ أَعۡبُدُ مَا تَعۡبُدُونَ

“Ba zan bauta wa abin da kuke bauta wa ba



Sura: Suratul Kafirun

Aya : 3

وَلَآ أَنتُمۡ عَٰبِدُونَ مَآ أَعۡبُدُ

“Ku kuma ba masu bautar abin da nake bauta wa ba ne



Sura: Suratul Kafirun

Aya : 4

وَلَآ أَنَا۠ عَابِدٞ مَّا عَبَدتُّمۡ

“Ni kuma ba mai bauta wa abin da kuka bauta wa ba ne



Sura: Suratul Kafirun

Aya : 5

وَلَآ أَنتُمۡ عَٰبِدُونَ مَآ أَعۡبُدُ

“Ku ma ba za ku bauta wa abin da nake bauta wa ba



Sura: Suratul Kafirun

Aya : 6

لَكُمۡ دِينُكُمۡ وَلِيَ دِينِ

“Addininku na gare ku, ni ma kuma addinina na gare ni[1].”


1- Annabi () ya ga wani yana karanta wannan Surar sai ya ce: “Amma dai wannan haqiqa ya kuvuta daga shirka”.