Sura: Suratu Maryam

Aya : 94

لَّقَدۡ أَحۡصَىٰهُمۡ وَعَدَّهُمۡ عَدّٗا

Lalle Ya kiyaye da su Ya kuma qididdige su sosai



Sura: Suratu Maryam

Aya : 95

وَكُلُّهُمۡ ءَاتِيهِ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِ فَرۡدًا

Kuma dukkansu kowa zai zo masa a ranar alqiyama shi kaxai



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 102

يَوۡمَ يُنفَخُ فِي ٱلصُّورِۚ وَنَحۡشُرُ ٱلۡمُجۡرِمِينَ يَوۡمَئِذٖ زُرۡقٗا

(Ita ce) ranar da za a busa qaho. Kuma Mu tayar da kafirai a wannan ranar idanuwansu jawur[1]


1- Watau saboda tsananin tsoro da fargaba.


Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 103

يَتَخَٰفَتُونَ بَيۡنَهُمۡ إِن لَّبِثۡتُمۡ إِلَّا عَشۡرٗا

Suna raxa a tsakaninsu (suna cewa): “Ba ku zauna (a qaburburanku) ba face (kwana) goma.”



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 104

نَّحۡنُ أَعۡلَمُ بِمَا يَقُولُونَ إِذۡ يَقُولُ أَمۡثَلُهُمۡ طَرِيقَةً إِن لَّبِثۡتُمۡ إِلَّا يَوۡمٗا

Mu Muka fi sanin abin da suke faxi lokacin da wanda ya fi tunani daga cikinsu yake cewa: “Ba ku zauna ba face rana guda.”



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 105

وَيَسۡـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلۡجِبَالِ فَقُلۡ يَنسِفُهَا رَبِّي نَسۡفٗا

Suna kuma tambayar ka game da duwatsu, to ka ce (da su): “Ubangijina zai niqe su tilis



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 106

فَيَذَرُهَا قَاعٗا صَفۡصَفٗا

“Sannan Ya bar ta (wato qasar) fili fetal



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 107

لَّا تَرَىٰ فِيهَا عِوَجٗا وَلَآ أَمۡتٗا

“Ba za ka ga wani kwari ko tudu a kanta ba.”



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 108

يَوۡمَئِذٖ يَتَّبِعُونَ ٱلدَّاعِيَ لَا عِوَجَ لَهُۥۖ وَخَشَعَتِ ٱلۡأَصۡوَاتُ لِلرَّحۡمَٰنِ فَلَا تَسۡمَعُ إِلَّا هَمۡسٗا

A wannan rana ne za su bi mai kira (zuwa matattara), ba mai bauxe masa; kuma (duk) muryoyi su yi qasa-qasa saboda (girman Allah) Mai rahama, sannan ba za ka ji (komai) ba sai raxa



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 109

يَوۡمَئِذٖ لَّا تَنفَعُ ٱلشَّفَٰعَةُ إِلَّا مَنۡ أَذِنَ لَهُ ٱلرَّحۡمَٰنُ وَرَضِيَ لَهُۥ قَوۡلٗا

A wannan ranar ceto ba ya amfani sai ga wanda (Allah) Mai rahama Ya yi wa izini, kuma Ya yarda da maganarsa



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 111

۞وَعَنَتِ ٱلۡوُجُوهُ لِلۡحَيِّ ٱلۡقَيُّومِۖ وَقَدۡ خَابَ مَنۡ حَمَلَ ظُلۡمٗا

Kuma dukkanin fuskoki suka qasqanta ga (Allah) Rayayye, Tsayayye (da Zatinsa). Haqiqa kuma duk wanda ya yo dakon zalunci ya tave



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 112

وَمَن يَعۡمَلۡ مِنَ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ وَهُوَ مُؤۡمِنٞ فَلَا يَخَافُ ظُلۡمٗا وَلَا هَضۡمٗا

Duk kuma wanda yake yin aiki na gari alhali kuwa shi mumini ne, to ba zai ji tsoron zalunci ba ko kuma qwauro



Sura: Suratul Anbiya

Aya : 47

وَنَضَعُ ٱلۡمَوَٰزِينَ ٱلۡقِسۡطَ لِيَوۡمِ ٱلۡقِيَٰمَةِ فَلَا تُظۡلَمُ نَفۡسٞ شَيۡـٔٗاۖ وَإِن كَانَ مِثۡقَالَ حَبَّةٖ مِّنۡ خَرۡدَلٍ أَتَيۡنَا بِهَاۗ وَكَفَىٰ بِنَا حَٰسِبِينَ

Za Mu kuma sanya ma’aunai na adalci a ranar alqiyama, sannan ba za a zalunci kowanne rai da komai ba, ko da ya zama gwargwadon qwayar komayya ne, za Mu zo da shi. Kuma Mun isa Masu hisabi!



Sura: Suratul Anbiya

Aya : 104

يَوۡمَ نَطۡوِي ٱلسَّمَآءَ كَطَيِّ ٱلسِّجِلِّ لِلۡكُتُبِۚ كَمَا بَدَأۡنَآ أَوَّلَ خَلۡقٖ نُّعِيدُهُۥۚ وَعۡدًا عَلَيۡنَآۚ إِنَّا كُنَّا فَٰعِلِينَ

(Ita ce) ranar da za Mu naxe sama kamar naxin marubuci ga takardu. Kamar yadda Muka qagi halitta da farko (haka) za Mu mai da ita. Wannan alqawari ne da Muka xauka. Lallai Mun kasance Masu aikata (haka)



Sura: Suratul Hajji

Aya : 1

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّاسُ ٱتَّقُواْ رَبَّكُمۡۚ إِنَّ زَلۡزَلَةَ ٱلسَّاعَةِ شَيۡءٌ عَظِيمٞ

Ya ku mutane, ku kiyaye dokokin Ubangijinku. Lalle girgizar (ranar) alqiyama abu ne mai girma



Sura: Suratul Hajji

Aya : 2

يَوۡمَ تَرَوۡنَهَا تَذۡهَلُ كُلُّ مُرۡضِعَةٍ عَمَّآ أَرۡضَعَتۡ وَتَضَعُ كُلُّ ذَاتِ حَمۡلٍ حَمۡلَهَا وَتَرَى ٱلنَّاسَ سُكَٰرَىٰ وَمَا هُم بِسُكَٰرَىٰ وَلَٰكِنَّ عَذَابَ ٱللَّهِ شَدِيدٞ

Ranar da za ku gan ta, (don tsananin firgita) kowacce mai shayarwa za ta manta da abin da ta shayar, kuma kowacce mai ciki ta zubar da cikinta, ka ga kuma mutane suna tangaxi, alhali kuwa ba bugaggu ba ne, sai dai azabar Allah ce mai tsanani



Sura: Suratul Hajji

Aya : 17

إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَٱلَّذِينَ هَادُواْ وَٱلصَّـٰبِـِٔينَ وَٱلنَّصَٰرَىٰ وَٱلۡمَجُوسَ وَٱلَّذِينَ أَشۡرَكُوٓاْ إِنَّ ٱللَّهَ يَفۡصِلُ بَيۡنَهُمۡ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِۚ إِنَّ ٱللَّهَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ شَهِيدٌ

Lalle waxanda suka yi imani da waxanda suka zama Yahudawa da Sabi’awa da waxanda suka zama Majusawa da kuma waxanda suka yi shirka, lalle Allah zai yi hukunci a tsakaninsu ranar alqiyama. Lalle Allah Mai ganin kowane abu ne



Sura: Suratul Hajji

Aya : 55

وَلَا يَزَالُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ فِي مِرۡيَةٖ مِّنۡهُ حَتَّىٰ تَأۡتِيَهُمُ ٱلسَّاعَةُ بَغۡتَةً أَوۡ يَأۡتِيَهُمۡ عَذَابُ يَوۡمٍ عَقِيمٍ

Waxanda kuwa suka kafirce ba za su daina kokwanton sa ba (watau Alqur’ani) har sai alqiyama ta zo musu ba zato ba tsammani, ko kuma azabar rana bakarara[1] ta zo musu


1- Watau ranar da kafirai ba za su samu wata rahama ko wani alheri ba.


Sura: Suratul Hajji

Aya : 56

ٱلۡمُلۡكُ يَوۡمَئِذٖ لِّلَّهِ يَحۡكُمُ بَيۡنَهُمۡۚ فَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ فِي جَنَّـٰتِ ٱلنَّعِيمِ

Mulki a wannan ranar na Allah ne, zai yi hukunci a tsakaninsu. To waxanda suka yi imani suka kuma yi kyawawan ayyuka, suna cikin gidajen Aljanna na ni’ima



Sura: Suratul Hajji

Aya : 69

ٱللَّهُ يَحۡكُمُ بَيۡنَكُمۡ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِ فِيمَا كُنتُمۡ فِيهِ تَخۡتَلِفُونَ

Allah zai yi hukunci a tsakaninku ranar alqiyama game da abin da kuka kasance kuna sassavawa a kansa



Sura: Suratul Mu’uminun

Aya : 16

ثُمَّ إِنَّكُمۡ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِ تُبۡعَثُونَ

Sannan kuma haqiqa za a tashe ku ranar Alqiyama



Sura: Suratun Nur

Aya : 24

يَوۡمَ تَشۡهَدُ عَلَيۡهِمۡ أَلۡسِنَتُهُمۡ وَأَيۡدِيهِمۡ وَأَرۡجُلُهُم بِمَا كَانُواْ يَعۡمَلُونَ

A ranar da harsunansu da hannayensu da kuma qafafunsu za su ba da shaida a kansu game da abin da suka kasance suna aikatawa



Sura: Suratun Nur

Aya : 25

يَوۡمَئِذٖ يُوَفِّيهِمُ ٱللَّهُ دِينَهُمُ ٱلۡحَقَّ وَيَعۡلَمُونَ أَنَّ ٱللَّهَ هُوَ ٱلۡحَقُّ ٱلۡمُبِينُ

A wannan ranar Allah zai ba su cikakken sakamakonsu na gaskiya kuma za su san cewa lalle Allah Shi ne gaskiya bayyananniya



Sura: Suratul Furqan

Aya : 22

يَوۡمَ يَرَوۡنَ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةَ لَا بُشۡرَىٰ يَوۡمَئِذٖ لِّلۡمُجۡرِمِينَ وَيَقُولُونَ حِجۡرٗا مَّحۡجُورٗا

Ranar da za su ga mala’iku[1] a wannan ranar babu wani farin ciki ga masu laifi, za kuma su riqa cewa: “(Albishir daga Allah) haramun ne abin haramtawa ne (a gare su)”


1- Watau ranar mutuwarsu ko a cikin qaburburansu da ranar da za a kora su domin yi musu hisabi.


Sura: Suratul Furqan

Aya : 23

وَقَدِمۡنَآ إِلَىٰ مَا عَمِلُواْ مِنۡ عَمَلٖ فَجَعَلۡنَٰهُ هَبَآءٗ مَّنثُورًا

Muka kuma gabato zuwa ga duk wani aiki da suka yi, sai Muka mai da shi qura abar xaixaitawa



Sura: Suratul Furqan

Aya : 24

أَصۡحَٰبُ ٱلۡجَنَّةِ يَوۡمَئِذٍ خَيۡرٞ مُّسۡتَقَرّٗا وَأَحۡسَنُ مَقِيلٗا

‘Yan Aljanna a wannan ranar su suka fi kyakkyawan mazauni kuma suka fi kyawon wurin barcin qailula[1]


1- Domin za a gama hisabi gabanin lokacin azahar, har ‘yan Aljanna za su shige ta su riski lokacin qailula a cikinta.


Sura: Suratul Furqan

Aya : 25

وَيَوۡمَ تَشَقَّقُ ٱلسَّمَآءُ بِٱلۡغَمَٰمِ وَنُزِّلَ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ تَنزِيلًا

Kuma (ka tuna) ranar da sama za ta kekkece da girgije, kuma a saukar da mala’iku gungu-gungu



Sura: Suratul Furqan

Aya : 26

ٱلۡمُلۡكُ يَوۡمَئِذٍ ٱلۡحَقُّ لِلرَّحۡمَٰنِۚ وَكَانَ يَوۡمًا عَلَى ٱلۡكَٰفِرِينَ عَسِيرٗا

Mulki tabbatacce a wannan ranar na (Allah) Mai rahama ne. Kuma ta kasance rana ce mawuyaciya ga kafurai



Sura: Suratul Furqan

Aya : 27

وَيَوۡمَ يَعَضُّ ٱلظَّالِمُ عَلَىٰ يَدَيۡهِ يَقُولُ يَٰلَيۡتَنِي ٱتَّخَذۡتُ مَعَ ٱلرَّسُولِ سَبِيلٗا

(Ka tuna) kuma ranar da azzalumi zai riqa cizon yatsunsa yana cewa: “Ina ma na bi hanya tare da Manzo!



Sura: Suratul Furqan

Aya : 28

يَٰوَيۡلَتَىٰ لَيۡتَنِي لَمۡ أَتَّخِذۡ فُلَانًا خَلِيلٗا

“Kaicona ina ma da ban riqi wane aboki ba!