Sura: Suratun Nazi’at

Aya : 41

فَإِنَّ ٱلۡجَنَّةَ هِيَ ٱلۡمَأۡوَىٰ

To lalle Aljanna ita ce makoma



Sura: Suratun Nazi’at

Aya : 42

يَسۡـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلسَّاعَةِ أَيَّانَ مُرۡسَىٰهَا

Suna tambayar ka game da alqiyama, yaushe ne lokacinta?



Sura: Suratun Nazi’at

Aya : 43

فِيمَ أَنتَ مِن ذِكۡرَىٰهَآ

Me ya gama ka da ambaton lokacinta?



Sura: Suratun Nazi’at

Aya : 44

إِلَىٰ رَبِّكَ مُنتَهَىٰهَآ

Zuwa ga Ubangijinka ne iyakacin saninta yake[1]


1- Watau Allah ne kaxai ya san lokacin aukuwarta.


Sura: Suratun Nazi’at

Aya : 45

إِنَّمَآ أَنتَ مُنذِرُ مَن يَخۡشَىٰهَا

Kai dai kawai mai gargaxin wanda yake tsoron ta ne



Sura: Suratun Nazi’at

Aya : 46

كَأَنَّهُمۡ يَوۡمَ يَرَوۡنَهَا لَمۡ يَلۡبَثُوٓاْ إِلَّا عَشِيَّةً أَوۡ ضُحَىٰهَا

Kai ka ce su ranar da za su gan ta ba su zauna ba (a duniya) face wani yammaci ko kuma hantsinta



Sura: Suratu Abasa

Aya : 33

فَإِذَا جَآءَتِ ٱلصَّآخَّةُ

Sannan idan mai sa kurunta ta zo (watau busa ta farko)



Sura: Suratu Abasa

Aya : 34

يَوۡمَ يَفِرُّ ٱلۡمَرۡءُ مِنۡ أَخِيهِ

A ranar da mutum yake guje wa xan’uwansa



Sura: Suratu Abasa

Aya : 35

وَأُمِّهِۦ وَأَبِيهِ

Da uwarsa da ubansa



Sura: Suratu Abasa

Aya : 36

وَصَٰحِبَتِهِۦ وَبَنِيهِ

Da matarsa da ‘ya’yansa



Sura: Suratu Abasa

Aya : 37

لِكُلِّ ٱمۡرِيٕٖ مِّنۡهُمۡ يَوۡمَئِذٖ شَأۡنٞ يُغۡنِيهِ

Kowane mutum daga cikinsu a wannan ranar yana da lamarin da ya sha kansa



Sura: Suratu Abasa

Aya : 38

وُجُوهٞ يَوۡمَئِذٖ مُّسۡفِرَةٞ

Wasu fuskoki a wannan ranar masu haske ne



Sura: Suratu Abasa

Aya : 39

ضَاحِكَةٞ مُّسۡتَبۡشِرَةٞ

Masu dariya, masu farin ciki



Sura: Suratu Abasa

Aya : 40

وَوُجُوهٞ يَوۡمَئِذٍ عَلَيۡهَا غَبَرَةٞ

Wasu fuskokin kuma a ranar akwai qura a kansu



Sura: Suratu Abasa

Aya : 41

تَرۡهَقُهَا قَتَرَةٌ

Baqin ciki zai lulluve su



Sura: Suratu Abasa

Aya : 42

أُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡكَفَرَةُ ٱلۡفَجَرَةُ

Waxannan su ne kafirai mavarnata



Sura: Suratul Infixar

Aya : 17

وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا يَوۡمُ ٱلدِّينِ

Kuma kai me ya sanar da kai mece ce ranar sakamako?



Sura: Suratul Infixar

Aya : 18

ثُمَّ مَآ أَدۡرَىٰكَ مَا يَوۡمُ ٱلدِّينِ

Sannan me ya sanar da kai mece ce ranar sakamako?



Sura: Suratul Infixar

Aya : 19

يَوۡمَ لَا تَمۡلِكُ نَفۡسٞ لِّنَفۡسٖ شَيۡـٔٗاۖ وَٱلۡأَمۡرُ يَوۡمَئِذٖ لِّلَّهِ

(Ita ce) ranar da wani rai ba ya mallakar wani amfani ga wani rai; al’amari kuwa (gaba xayansa) a wannan ranar yana ga Allah



Sura: Suratul Fajr

Aya : 21

كَلَّآۖ إِذَا دُكَّتِ ٱلۡأَرۡضُ دَكّٗا دَكّٗا

Ba haka ne ba, idan aka girgiza qasa matuqar girgiza



Sura: Suratul Fajr

Aya : 22

وَجَآءَ رَبُّكَ وَٱلۡمَلَكُ صَفّٗا صَفّٗا

Ubangijinka kuma Ya zo[1] tare da mala’iku sahu-sahu


1- Watau don yin hukunci a tsakanin bayinsa.


Sura: Suratul Fajr

Aya : 23

وَجِاْيٓءَ يَوۡمَئِذِۭ بِجَهَنَّمَۚ يَوۡمَئِذٖ يَتَذَكَّرُ ٱلۡإِنسَٰنُ وَأَنَّىٰ لَهُ ٱلذِّكۡرَىٰ

Aka kuma zo da Jahannama a wannan ranar. To fa a wannan ranar ne mutum zai tuna (sakacinsa), ta yaya wannan tunawar za ta yi masa amfani?



Sura: Suratul Fajr

Aya : 24

يَقُولُ يَٰلَيۡتَنِي قَدَّمۡتُ لِحَيَاتِي

Zai ce: “Kaitona, ina ma da na gabatar (da ayyukan alheri) a rayuwata!”



Sura: Suratul Fajr

Aya : 25

فَيَوۡمَئِذٖ لَّا يُعَذِّبُ عَذَابَهُۥٓ أَحَدٞ

To a wannan ranar ba wani xaya da zai yi azaba irin azabarsa (watau Allah)



Sura: Suratul Fajr

Aya : 26

وَلَا يُوثِقُ وَثَاقَهُۥٓ أَحَدٞ

Ba kuma xaya da zai yi xauri irin xaurinsa



Sura: Suratul Fajr

Aya : 27

يَـٰٓأَيَّتُهَا ٱلنَّفۡسُ ٱلۡمُطۡمَئِنَّةُ

(Za a ce): Ya kai wannan rai mai nutsuwa



Sura: Suratul Fajr

Aya : 28

ٱرۡجِعِيٓ إِلَىٰ رَبِّكِ رَاضِيَةٗ مَّرۡضِيَّةٗ

Ka koma zuwa ga Ubangijinka kana mai yarda (da sakamako), abin yarda



Sura: Suratul Fajr

Aya : 29

فَٱدۡخُلِي فِي عِبَٰدِي

Don haka ka shiga cikin bayina



Sura: Suratul Fajr

Aya : 30

وَٱدۡخُلِي جَنَّتِي

Ka kuma shiga Aljannata



Sura: Suratuz Zalzala

Aya : 1

إِذَا زُلۡزِلَتِ ٱلۡأَرۡضُ زِلۡزَالَهَا

Idan aka girgiza qasa matuqar girgiza ta