Sura: Suratu Hud

Aya : 70

فَلَمَّا رَءَآ أَيۡدِيَهُمۡ لَا تَصِلُ إِلَيۡهِ نَكِرَهُمۡ وَأَوۡجَسَ مِنۡهُمۡ خِيفَةٗۚ قَالُواْ لَا تَخَفۡ إِنَّآ أُرۡسِلۡنَآ إِلَىٰ قَوۡمِ لُوطٖ

To lokacin da ya ga hannayensu ba sa isa gare shi (soyayyen xan maraqin), sai ya shiga yin xari-xari da su[1], kuma ya voye jin tsoronsu a zuciyarsa, suka ce: “Kar ka tsorata; mu an aiko mu ne zuwa ga mutanen Luxu.”


1- Idan baqo ya ci abincin da aka kawo masa wannan yakan sanya nutsuwa a zukatan masu gida da yarda da shi.


Sura: Suratu Hud

Aya : 71

وَٱمۡرَأَتُهُۥ قَآئِمَةٞ فَضَحِكَتۡ فَبَشَّرۡنَٰهَا بِإِسۡحَٰقَ وَمِن وَرَآءِ إِسۡحَٰقَ يَعۡقُوبَ

Matarsa kuwa tana tsaye sai ta yi dariya, sai Muka yi mata albishir da Is’haqa, bayan kuma Is’haqa (sai) Yakubu



Sura: Suratu Hud

Aya : 72

قَالَتۡ يَٰوَيۡلَتَىٰٓ ءَأَلِدُ وَأَنَا۠ عَجُوزٞ وَهَٰذَا بَعۡلِي شَيۡخًاۖ إِنَّ هَٰذَا لَشَيۡءٌ عَجِيبٞ

Ta ce: “Kaicona! Yanzu zan iya haihuwa, ga ni tsohuwa kuma ga mijina nan ma tsoho? Lalle wannan abin mamaki ne!”



Sura: Suratu Hud

Aya : 73

قَالُوٓاْ أَتَعۡجَبِينَ مِنۡ أَمۡرِ ٱللَّهِۖ رَحۡمَتُ ٱللَّهِ وَبَرَكَٰتُهُۥ عَلَيۡكُمۡ أَهۡلَ ٱلۡبَيۡتِۚ إِنَّهُۥ حَمِيدٞ مَّجِيدٞ

Suka ce: “Yanzu kya riqa mamaki game da al’amarin Allah? Rahamar Allah da albarkarsa su tabbata a gare ku mutanen wannan gidan. Lalle shi (Allah) Sha-yabo ne Mai girma.”



Sura: Suratu Hud

Aya : 74

فَلَمَّا ذَهَبَ عَنۡ إِبۡرَٰهِيمَ ٱلرَّوۡعُ وَجَآءَتۡهُ ٱلۡبُشۡرَىٰ يُجَٰدِلُنَا فِي قَوۡمِ لُوطٍ

To lokacin da tsoro ya rabu da Ibrahimu, kuma albishir ya zo masa, (sai ya zama) yana muhawara da Mu[1] game da mutanen Luxu


1- Watau yana muhawara da mala’ikun Allah.


Sura: Suratu Hud

Aya : 75

إِنَّ إِبۡرَٰهِيمَ لَحَلِيمٌ أَوَّـٰهٞ مُّنِيبٞ

Lalle Ibrahimu tabbas mai haquri ne mai yawan ambato Allah mai yawan komawa gare Shi



Sura: Suratu Hud

Aya : 76

يَـٰٓإِبۡرَٰهِيمُ أَعۡرِضۡ عَنۡ هَٰذَآۖ إِنَّهُۥ قَدۡ جَآءَ أَمۡرُ رَبِّكَۖ وَإِنَّهُمۡ ءَاتِيهِمۡ عَذَابٌ غَيۡرُ مَرۡدُودٖ

Ya kai Ibrahimu, ka kau da kai daga wannan. Lalle umarnin Ubangijinka ya zo; lalle kuwa azaba wadda ba mai kawar da ita za ta zo musu



Sura: Suratu Ibrahim

Aya : 35

وَإِذۡ قَالَ إِبۡرَٰهِيمُ رَبِّ ٱجۡعَلۡ هَٰذَا ٱلۡبَلَدَ ءَامِنٗا وَٱجۡنُبۡنِي وَبَنِيَّ أَن نَّعۡبُدَ ٱلۡأَصۡنَامَ

(Ka tuna) kuma lokacin da Ibrahimu ya ce: “Ya Ubangijina, Ka sanya wannan gari (Makka) ya zama amintacce, kuma Ka nesantar da ni da ‘ya’yana daga bauta wa gumaka



Sura: Suratu Ibrahim

Aya : 36

رَبِّ إِنَّهُنَّ أَضۡلَلۡنَ كَثِيرٗا مِّنَ ٱلنَّاسِۖ فَمَن تَبِعَنِي فَإِنَّهُۥ مِنِّيۖ وَمَنۡ عَصَانِي فَإِنَّكَ غَفُورٞ رَّحِيمٞ

“Ya Ubangijina, lalle su (gumakan) sun vatar da mutane masu yawa; wanda kuwa ya bi ni to lalle shi yana tare da ni; wanda kuma ya sava mini to lalle Kai Mai gafara ne, Mai jin qai.”



Sura: Suratu Ibrahim

Aya : 37

رَّبَّنَآ إِنِّيٓ أَسۡكَنتُ مِن ذُرِّيَّتِي بِوَادٍ غَيۡرِ ذِي زَرۡعٍ عِندَ بَيۡتِكَ ٱلۡمُحَرَّمِ رَبَّنَا لِيُقِيمُواْ ٱلصَّلَوٰةَ فَٱجۡعَلۡ أَفۡـِٔدَةٗ مِّنَ ٱلنَّاسِ تَهۡوِيٓ إِلَيۡهِمۡ وَٱرۡزُقۡهُم مِّنَ ٱلثَّمَرَٰتِ لَعَلَّهُمۡ يَشۡكُرُونَ

“Ya Ubangijinmu, lalle ni na zaunar da wasu daga zuriyata a wani kwari wanda ba a shuka a cikinsa[1] kusa da Xakinka mai alfarma; ya Ubangijinmu don su tsai da salla, to Ka sanya zukatan mutane su riqa karkatowa zuwa gare su, kuma Ka arzuta su da ‘ya’yan itace don su gode (maka)


1- Watau kuyangarsa Hajara () da xansa Isma’ilu (). Ya zaunar da su garin Makka da izinin Allah ().


Sura: Suratu Ibrahim

Aya : 38

رَبَّنَآ إِنَّكَ تَعۡلَمُ مَا نُخۡفِي وَمَا نُعۡلِنُۗ وَمَا يَخۡفَىٰ عَلَى ٱللَّهِ مِن شَيۡءٖ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَلَا فِي ٱلسَّمَآءِ

“Ya Ubangijinmu, lalle Kai Ka san abin da muke voyewa da abin da muke bayyanawa. Babu wani abu a cikin qasa ko a cikin sama da zai vuya ga Allah



Sura: Suratu Ibrahim

Aya : 39

ٱلۡحَمۡدُ لِلَّهِ ٱلَّذِي وَهَبَ لِي عَلَى ٱلۡكِبَرِ إِسۡمَٰعِيلَ وَإِسۡحَٰقَۚ إِنَّ رَبِّي لَسَمِيعُ ٱلدُّعَآءِ

“Dukkan yabo ya tabbata ga Allah wanda Ya ba ni Isma’ila da Is’haqa a cikin halin tsufa. Lalle Ubangijina tabbas Mai jin roqo ne



Sura: Suratu Ibrahim

Aya : 40

رَبِّ ٱجۡعَلۡنِي مُقِيمَ ٱلصَّلَوٰةِ وَمِن ذُرِّيَّتِيۚ رَبَّنَا وَتَقَبَّلۡ دُعَآءِ

“Ya Ubangijina, Ka sanya ni in zama mai tsayar da salla da kuma zuriyata. Ya Ubangijinmu, Ka karvi addu’ata



Sura: Suratu Ibrahim

Aya : 41

رَبَّنَا ٱغۡفِرۡ لِي وَلِوَٰلِدَيَّ وَلِلۡمُؤۡمِنِينَ يَوۡمَ يَقُومُ ٱلۡحِسَابُ

“Ya Ubangijinmu Ka gafarta mini, ni da iyayena da kuma muminai ranar da hisabi zai kankama.”



Sura: Suratul Hijr

Aya : 51

وَنَبِّئۡهُمۡ عَن ضَيۡفِ إِبۡرَٰهِيمَ

Kuma ka ba su labari game da baqin Ibrahimu[1]


1- Su ne mala’ikun da suka ziyarci Ibrahim () a kan hanyarsu ta zuwa hallaka mutanen Annabi Luxu ().


Sura: Suratul Hijr

Aya : 52

إِذۡ دَخَلُواْ عَلَيۡهِ فَقَالُواْ سَلَٰمٗا قَالَ إِنَّا مِنكُمۡ وَجِلُونَ

Lokacin da suka shiga wurinsa suka ce: “Muna yi maka sallama”, ya ce: “Lalle mu a tsorace muke da ku.”



Sura: Suratul Hijr

Aya : 53

قَالُواْ لَا تَوۡجَلۡ إِنَّا نُبَشِّرُكَ بِغُلَٰمٍ عَلِيمٖ

Suka ce: “Kada ka ji tsoro, lalle mu muna yi maka albishir ne da (samun) yaro mai ilimi.”



Sura: Suratul Hijr

Aya : 54

قَالَ أَبَشَّرۡتُمُونِي عَلَىٰٓ أَن مَّسَّنِيَ ٱلۡكِبَرُ فَبِمَ تُبَشِّرُونَ

Ya ce: “Yanzu kwa yi mini albishir bayan kuwa ga shi tsufa ya kama ni? To da me kuma za ku yi min albishir?!”



Sura: Suratul Hijr

Aya : 55

قَالُواْ بَشَّرۡنَٰكَ بِٱلۡحَقِّ فَلَا تَكُن مِّنَ ٱلۡقَٰنِطِينَ

Suka ce: “Mun yi maka albishir da gaskiya ne, don haka kada ka zamo daga masu xebe qauna.”



Sura: Suratul Hijr

Aya : 56

قَالَ وَمَن يَقۡنَطُ مِن رَّحۡمَةِ رَبِّهِۦٓ إِلَّا ٱلضَّآلُّونَ

Ya ce: “Ba wanda zai xebe qauna daga rahamar Ubangijinsa, sai vatattun (mutane).”



Sura: Suratun Nahl

Aya : 120

إِنَّ إِبۡرَٰهِيمَ كَانَ أُمَّةٗ قَانِتٗا لِّلَّهِ حَنِيفٗا وَلَمۡ يَكُ مِنَ ٱلۡمُشۡرِكِينَ

Lalle Ibrahimu ya zama abin koyi ne mai biyayya ga Allah mai kauce wa varna, bai kuma zamanto daga masu shirka ba



Sura: Suratun Nahl

Aya : 121

شَاكِرٗا لِّأَنۡعُمِهِۚ ٱجۡتَبَىٰهُ وَهَدَىٰهُ إِلَىٰ صِرَٰطٖ مُّسۡتَقِيمٖ

Mai godiya ne ga ni’imarsa (wato Allah), Ya zave shi, Ya kuma shirye shi zuwa ga tafarki madaidaici



Sura: Suratun Nahl

Aya : 122

وَءَاتَيۡنَٰهُ فِي ٱلدُّنۡيَا حَسَنَةٗۖ وَإِنَّهُۥ فِي ٱلۡأٓخِرَةِ لَمِنَ ٱلصَّـٰلِحِينَ

Mun kuma ba shi kyakkyawa a duniya; lalle kuma shi a lahira tabbas yana daga cikin salihai



Sura: Suratu Maryam

Aya : 41

وَٱذۡكُرۡ فِي ٱلۡكِتَٰبِ إِبۡرَٰهِيمَۚ إِنَّهُۥ كَانَ صِدِّيقٗا نَّبِيًّا

Kuma ka ambaci (labarin) Ibrahimu a cikin (wannan) littafi (Alqur’ani). Lalle shi mutum ne mai yawan gaskiya (kuma) Annabi



Sura: Suratu Maryam

Aya : 42

إِذۡ قَالَ لِأَبِيهِ يَـٰٓأَبَتِ لِمَ تَعۡبُدُ مَا لَا يَسۡمَعُ وَلَا يُبۡصِرُ وَلَا يُغۡنِي عَنكَ شَيۡـٔٗا

Lokacin da ya ce da Babansa: “Ya Babana, me ya sa kake bauta wa abin da ba ya ji ba kuma ya gani, kuma ba ya yi maka maganin komai?



Sura: Suratu Maryam

Aya : 43

يَـٰٓأَبَتِ إِنِّي قَدۡ جَآءَنِي مِنَ ٱلۡعِلۡمِ مَا لَمۡ يَأۡتِكَ فَٱتَّبِعۡنِيٓ أَهۡدِكَ صِرَٰطٗا سَوِيّٗا

“Ya Babana, Lalle ni haqiqa wani ilimi ya zo mini wanda kai bai zo maka ba, to ka bi ni zan shiryar da kai hanya madaidaiciya



Sura: Suratu Maryam

Aya : 44

يَـٰٓأَبَتِ لَا تَعۡبُدِ ٱلشَّيۡطَٰنَۖ إِنَّ ٱلشَّيۡطَٰنَ كَانَ لِلرَّحۡمَٰنِ عَصِيّٗا

“Ya Babana, kada ka bauta wa Shaixan ; lalle Shaixan ya kasance mai savo ne ga (Allah) Mai rahama



Sura: Suratu Maryam

Aya : 45

يَـٰٓأَبَتِ إِنِّيٓ أَخَافُ أَن يَمَسَّكَ عَذَابٞ مِّنَ ٱلرَّحۡمَٰنِ فَتَكُونَ لِلشَّيۡطَٰنِ وَلِيّٗا

“Ya Babana, lalle ni fa ina tsoron azaba ta shafe ka daga (Allah) Mai rahama, sai ka zama majivincin Shaixan.”



Sura: Suratu Maryam

Aya : 46

قَالَ أَرَاغِبٌ أَنتَ عَنۡ ءَالِهَتِي يَـٰٓإِبۡرَٰهِيمُۖ لَئِن لَّمۡ تَنتَهِ لَأَرۡجُمَنَّكَۖ وَٱهۡجُرۡنِي مَلِيّٗا

(Babansa) ya ce: “Yanzu Ibrahimu qyamar iyayen gijina kake yi? To tabbas idan ba ka bari ba lalle zan jefe ka; ka vace min da gani na tsawon lokaci!”



Sura: Suratu Maryam

Aya : 47

قَالَ سَلَٰمٌ عَلَيۡكَۖ سَأَسۡتَغۡفِرُ لَكَ رَبِّيٓۖ إِنَّهُۥ كَانَ بِي حَفِيّٗا

(Annabi Ibrahimu) ya ce: “Aminci ya tabbata gare ka; zan nema maka gafarar Ubangijina[1]; don ko lalle Shi ya tabbata Mai haba-haba ne da ni


1- Ya faxi haka ne kafin Allah ya hana shi nema masa gafara.