Sura: Suratul An’am

Aya : 85

وَزَكَرِيَّا وَيَحۡيَىٰ وَعِيسَىٰ وَإِلۡيَاسَۖ كُلّٞ مِّنَ ٱلصَّـٰلِحِينَ

Da Zakariyya da Yahaya da Isa da Iliyasu; kowanne daga cikinsu yana cikin salihan bayi



Sura: Suratus Saffat

Aya : 123

وَإِنَّ إِلۡيَاسَ لَمِنَ ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Kuma lalle Ilyasu tabbas yana daga cikin manzanni



Sura: Suratus Saffat

Aya : 124

إِذۡ قَالَ لِقَوۡمِهِۦٓ أَلَا تَتَّقُونَ

Lokacin da ya ce da mutanensa: “Yanzu ba za ku kiyaye dokokin (Allah) ba?



Sura: Suratus Saffat

Aya : 125

أَتَدۡعُونَ بَعۡلٗا وَتَذَرُونَ أَحۡسَنَ ٱلۡخَٰلِقِينَ

“Yanzu kwa riqa bauta wa (gunkin) Ba’alu ku riqa barin Mafi iya kyautata halitta?



Sura: Suratus Saffat

Aya : 126

ٱللَّهَ رَبَّكُمۡ وَرَبَّ ءَابَآئِكُمُ ٱلۡأَوَّلِينَ

“(Wato) Allah Ubangijinku kuma Ubangijin iyayenku na farko?”



Sura: Suratus Saffat

Aya : 127

فَكَذَّبُوهُ فَإِنَّهُمۡ لَمُحۡضَرُونَ

Sai suka qaryata shi, to don haka, lalle za a halarto da su (wuta)



Sura: Suratus Saffat

Aya : 128

إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلۡمُخۡلَصِينَ

Sai dai bayin Allah waxanda aka tsarkake



Sura: Suratus Saffat

Aya : 129

وَتَرَكۡنَا عَلَيۡهِ فِي ٱلۡأٓخِرِينَ

Muka kuma bar (kyakkyawan yabo) a gare shi ga ‘yan baya



Sura: Suratus Saffat

Aya : 130

سَلَٰمٌ عَلَىٰٓ إِلۡ يَاسِينَ

Aminci ya tabbata ga Ilyasu



Sura: Suratus Saffat

Aya : 131

إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجۡزِي ٱلۡمُحۡسِنِينَ

Lalle Mu kamar haka Muke saka wa masu kyautatawa



Sura: Suratus Saffat

Aya : 132

إِنَّهُۥ مِنۡ عِبَادِنَا ٱلۡمُؤۡمِنِينَ

Lalle shi yana daga bayinmu muminai