Sura: Suratux Xariq

Aya : 8

إِنَّهُۥ عَلَىٰ رَجۡعِهِۦ لَقَادِرٞ

Lalle Shi (Allah) Mai iko ne a kan dawo da shi



Sura: Suratul A’ala

Aya : 7

إِلَّا مَا شَآءَ ٱللَّهُۚ إِنَّهُۥ يَعۡلَمُ ٱلۡجَهۡرَ وَمَا يَخۡفَىٰ

Sai abin da Allah Ya ga dama, Lalle Shi Yana sane da bayyanannen (abu) da kuma abin da yake vuya



Sura: Suratud Dhuha

Aya : 11

وَأَمَّا بِنِعۡمَةِ رَبِّكَ فَحَدِّثۡ

Amma kuma game da ni’imar Ubangijinka sai ka ba da labari



Sura: Suratul Alaq

Aya : 14

أَلَمۡ يَعۡلَم بِأَنَّ ٱللَّهَ يَرَىٰ

Shin bai sani ba cewa lalle Allah Yana ganin (sa)?



Sura: Suratul Bayyina

Aya : 5

وَمَآ أُمِرُوٓاْ إِلَّا لِيَعۡبُدُواْ ٱللَّهَ مُخۡلِصِينَ لَهُ ٱلدِّينَ حُنَفَآءَ وَيُقِيمُواْ ٱلصَّلَوٰةَ وَيُؤۡتُواْ ٱلزَّكَوٰةَۚ وَذَٰلِكَ دِينُ ٱلۡقَيِّمَةِ

Ba a kuma umarce su ba sai don su bauta wa Allah suna masu tsantsanta addini gare Shi, suna masu kauce wa varna, suna kuma tsayar da salla, kuma suna ba da zakka. Wannan kuwa shi ne addinin miqaqqiyar hanya



Sura: Suratun Nasr

Aya : 3

فَسَبِّحۡ بِحَمۡدِ رَبِّكَ وَٱسۡتَغۡفِرۡهُۚ إِنَّهُۥ كَانَ تَوَّابَۢا

To ka yi tasbihi da yabon Ubangijinka, ka kuma nemi gafararsa. Lalle Shi Ya kasance Mai karvar tuba ne



Sura: Suratul Ikhlas

Aya : 1

قُلۡ هُوَ ٱللَّهُ أَحَدٌ

Ka ce: “Shi Allah Xaya ne[1]


1- Watau a Zatinsa da siffofinsa da ayyukansa, kuma shi kaxai ya cancanci a bauta masa.


Sura: Suratul Ikhlas

Aya : 2

ٱللَّهُ ٱلصَّمَدُ

“Allah Abin nufa da buqatu[1]


1- Watau wanda shugabanci ya tuqe zuwa gare shi, domin ya tattara dukkan siffofin kamala da xaukaka.


Sura: Suratul Ikhlas

Aya : 3

لَمۡ يَلِدۡ وَلَمۡ يُولَدۡ

“Bai haifa ba, kuma ba a haife Shi ba



Sura: Suratul Ikhlas

Aya : 4

وَلَمۡ يَكُن لَّهُۥ كُفُوًا أَحَدُۢ

“Kuma babu wani da ya kasance kini a gare Shi[1].”


1- Domin babu mai kama da shi a sunayensa da siffofinsa da ayyukansa.


Sura: Suratun Nas

Aya : 2

مَلِكِ ٱلنَّاسِ

“Sarkin mutane