Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 111

۞قَالُوٓاْ أَنُؤۡمِنُ لَكَ وَٱتَّبَعَكَ ٱلۡأَرۡذَلُونَ

Suka ce: “Yanzu ma yi imani da kai alhali qasqantattu ne mabiyanka?”



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 112

قَالَ وَمَا عِلۡمِي بِمَا كَانُواْ يَعۡمَلُونَ

Ya ce: “Ba ni da sani game da abin da suka zamanto suna aikatawa



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 113

إِنۡ حِسَابُهُمۡ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّيۖ لَوۡ تَشۡعُرُونَ

“Hisabinsu kawai yana wajen Ubangijina ne; da za ku gane



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 114

وَمَآ أَنَا۠ بِطَارِدِ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ

“Ni kuma ba mai korar muminai ba ne



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 115

إِنۡ أَنَا۠ إِلَّا نَذِيرٞ مُّبِينٞ

“Ni kawai mai gargaxi ne mai bayyanawa.”



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 116

قَالُواْ لَئِن لَّمۡ تَنتَهِ يَٰنُوحُ لَتَكُونَنَّ مِنَ ٱلۡمَرۡجُومِينَ

Suka ce: “Ya Nuhu, mun rantse idan ba ka daina (faxar abin da kake faxa) ba, tabbas za ka zamanto daga cikin jefaffu!”



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 117

قَالَ رَبِّ إِنَّ قَوۡمِي كَذَّبُونِ

Ya ce: “Ya Ubangijina, lalle mutanena sun qaryata ni



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 118

فَٱفۡتَحۡ بَيۡنِي وَبَيۡنَهُمۡ فَتۡحٗا وَنَجِّنِي وَمَن مَّعِيَ مِنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ

“Ka yi hukunci tsakanina da su, kuma Ka tserar da ni tare da muminan da suke tare da ni.”



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 119

فَأَنجَيۡنَٰهُ وَمَن مَّعَهُۥ فِي ٱلۡفُلۡكِ ٱلۡمَشۡحُونِ

Sai Muka tserar da shi da waxanda suke tare da shi a cikin jirgin ruwan da ke maqare (da mutane da dabbobi)



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 120

ثُمَّ أَغۡرَقۡنَا بَعۡدُ ٱلۡبَاقِينَ

Sannan bayan haka Muka nutsar da sauran



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 121

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ

Lalle a game da wannan tabbas akwai aya; kuma yawancinsu ba su zamanto muminai ba



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 122

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

Kuma lalle Ubangijinka tabbas Shi ne Mabuwayi, Mai jin qai



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 123

كَذَّبَتۡ عَادٌ ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Adawa (ma) sun qaryata manzanni[1]


1- Domin qaryata Annabi Hudu () daidai yake da qaryata duk manzannin Allah, saboda saqo iri xaya suke xauke da shi.


Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 124

إِذۡ قَالَ لَهُمۡ أَخُوهُمۡ هُودٌ أَلَا تَتَّقُونَ

Lokacin da xan’uwansu Hudu ya ce da su: “Yanzu ba kwa riqa kiyaye dokokin (Allah) ba?



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 125

إِنِّي لَكُمۡ رَسُولٌ أَمِينٞ

“Lalle ni Manzo ne amintacce gare ku



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 126

فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

“To ku kiyaye dokokin Allah kuma ku bi ni



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 127

وَمَآ أَسۡـَٔلُكُمۡ عَلَيۡهِ مِنۡ أَجۡرٍۖ إِنۡ أَجۡرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

“Kuma ba na tambayar ku wani lada game da shi (isar da manzancin); ladana yana wajen Ubangijin talikai kawai



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 128

أَتَبۡنُونَ بِكُلِّ رِيعٍ ءَايَةٗ تَعۡبَثُونَ

“Yanzu kwa riqa yin dogayen gine-gine a kan tuddai kuna sharholiya?



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 129

وَتَتَّخِذُونَ مَصَانِعَ لَعَلَّكُمۡ تَخۡلُدُونَ

“Kuma ku riqa gina ganuwoyi da maka-makan gidaje kamar za ku dawwama?



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 130

وَإِذَا بَطَشۡتُم بَطَشۡتُمۡ جَبَّارِينَ

“Idan kuma kuka yi damqa sai kukan yi damqa da tsanani



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 131

فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

“To ku kiyaye dokokin Allah kuma ku bi ni



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 132

وَٱتَّقُواْ ٱلَّذِيٓ أَمَدَّكُم بِمَا تَعۡلَمُونَ

“Kuma ku kiyaye dokokin (Allah) wanda Ya ni’imta ku da abin da kuka sani



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 133

أَمَدَّكُم بِأَنۡعَٰمٖ وَبَنِينَ

“Ya ni’imta ku da dabbobin ni’ima da ‘ya’ya



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 134

وَجَنَّـٰتٖ وَعُيُونٍ

“Da kuma gonakai da idanuwan ruwa



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 135

إِنِّيٓ أَخَافُ عَلَيۡكُمۡ عَذَابَ يَوۡمٍ عَظِيمٖ

“Lalle ni ina jiye muku tsoron azabar wani yini mai girma.”



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 136

قَالُواْ سَوَآءٌ عَلَيۡنَآ أَوَعَظۡتَ أَمۡ لَمۡ تَكُن مِّنَ ٱلۡوَٰعِظِينَ

Suka ce: “Mu duk xaya ne a wajenmu; ko ka yi wa’azi ko kuwa kada ka zamanto daga masu wa’azi



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 137

إِنۡ هَٰذَآ إِلَّا خُلُقُ ٱلۡأَوَّلِينَ

“Wannan ba wani abu ba ne in ban da halayyar mutanen farko



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 138

وَمَا نَحۡنُ بِمُعَذَّبِينَ

“Mu kuma ba waxanda za a yi wa azaba ba ne.”



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 139

فَكَذَّبُوهُ فَأَهۡلَكۡنَٰهُمۡۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ

Sai suka qaryata shi, sannan Muka hallaka su. Lalle a game da wannan tabbas akwai aya; kuma yawancinsu ba su zamanto muminai ba



Sura: Suratus Shu’ara

Aya : 140

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

Kuma lalle Ubangijinka tabbas Shi ne Mabuwayi, Mai jin qai