Sura: Suratul Mursalat

Aya : 6

عُذۡرًا أَوۡ نُذۡرًا

Don yanke hanzari ko don gargaxi



Sura: Suratul Mursalat

Aya : 7

إِنَّمَا تُوعَدُونَ لَوَٰقِعٞ

Lalle abin da ake yi muku alqawari tabbas mai afkuwa ne



Sura: Suratul Mursalat

Aya : 8

فَإِذَا ٱلنُّجُومُ طُمِسَتۡ

To idan taurari aka shafe haskensu



Sura: Suratul Mursalat

Aya : 9

وَإِذَا ٱلسَّمَآءُ فُرِجَتۡ

Idan kuma sama aka tsattsage ta



Sura: Suratul Mursalat

Aya : 10

وَإِذَا ٱلۡجِبَالُ نُسِفَتۡ

Idan kuma duwatsu aka sheqe su



Sura: Suratul Mursalat

Aya : 11

وَإِذَا ٱلرُّسُلُ أُقِّتَتۡ

Idan kuma manzanni aka tattara su[1]


1- Watau don su ba da shaida cewa sun isar wa al’ummunnsu saqon Allah.


Sura: Suratul Mursalat

Aya : 12

لِأَيِّ يَوۡمٍ أُجِّلَتۡ

Ga wacce rana ce aka qayyaje musu



Sura: Suratul Mursalat

Aya : 13

لِيَوۡمِ ٱلۡفَصۡلِ

Ga rana ta yin hukunci[1]


1- Watau hukunci tsakanin bayi, a bayyana mai gaskiya da marar gaskiya da xan wuta da xan Aljanna.


Sura: Suratul Mursalat

Aya : 14

وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا يَوۡمُ ٱلۡفَصۡلِ

Me kuma ya sanar da kai ranar yin hukunci



Sura: Suratul Mursalat

Aya : 15

وَيۡلٞ يَوۡمَئِذٖ لِّلۡمُكَذِّبِينَ

Tsananin azaba ya tabbata a wannan ranar ga masu qaryatawa



Sura: Suratul Mursalat

Aya : 16

أَلَمۡ نُهۡلِكِ ٱلۡأَوَّلِينَ

Yanzu ba Mu hallakar da na farko ba?



Sura: Suratul Mursalat

Aya : 17

ثُمَّ نُتۡبِعُهُمُ ٱلۡأٓخِرِينَ

Sannan Muka biyo su da na qarshe?



Sura: Suratul Mursalat

Aya : 18

كَذَٰلِكَ نَفۡعَلُ بِٱلۡمُجۡرِمِينَ

Kamar haka Muke yi wa masu manyan laifuka



Sura: Suratul Mursalat

Aya : 19

وَيۡلٞ يَوۡمَئِذٖ لِّلۡمُكَذِّبِينَ

Tsananin azaba ya tabbata a wannan ranar ga masu qaryatawa



Sura: Suratul Mursalat

Aya : 20

أَلَمۡ نَخۡلُقكُّم مِّن مَّآءٖ مَّهِينٖ

Yanzu ba Mu halicce ku daga wani wulaqantaccen ruwa ba?



Sura: Suratul Mursalat

Aya : 21

فَجَعَلۡنَٰهُ فِي قَرَارٖ مَّكِينٍ

Sannan Muka sanya shi cikin matabbata mai aminci?



Sura: Suratul Mursalat

Aya : 22

إِلَىٰ قَدَرٖ مَّعۡلُومٖ

Zuwa wani lokaci sananne?



Sura: Suratul Mursalat

Aya : 23

فَقَدَرۡنَا فَنِعۡمَ ٱلۡقَٰدِرُونَ

Sannan Muka qaddara (komai ta yadda ya dace)? To madalla da Masu qaddarawa



Sura: Suratul Mursalat

Aya : 24

وَيۡلٞ يَوۡمَئِذٖ لِّلۡمُكَذِّبِينَ

Tsananin azaba ya tabbata a wannan ranar ga masu qaryatawa



Sura: Suratul Mursalat

Aya : 25

أَلَمۡ نَجۡعَلِ ٱلۡأَرۡضَ كِفَاتًا

Yanzu ba Mu sanya qasa (ta zama) matattara ba?



Sura: Suratul Mursalat

Aya : 26

أَحۡيَآءٗ وَأَمۡوَٰتٗا

(Ga) rayayyu da matattu[1]?


1- Watau masu rai a cikin gidajensu a bayanta, matatu kuma a binne a cikin qaburburansu a qarqashinta.


Sura: Suratul Mursalat

Aya : 27

وَجَعَلۡنَا فِيهَا رَوَٰسِيَ شَٰمِخَٰتٖ وَأَسۡقَيۡنَٰكُم مَّآءٗ فُرَاتٗا

Muka kuma sanya kafaffun duwatsu dogaye a cikinta, Muka kuma shayar da ku ruwa mai daxi?



Sura: Suratul Mursalat

Aya : 28

وَيۡلٞ يَوۡمَئِذٖ لِّلۡمُكَذِّبِينَ

Tsananin azaba ya tabbata a wannan ranar ga masu qaryatawa



Sura: Suratul Mursalat

Aya : 29

ٱنطَلِقُوٓاْ إِلَىٰ مَا كُنتُم بِهِۦ تُكَذِّبُونَ

Ku tafi zuwa ga abin da kuka kasance kuna qaryatawa



Sura: Suratul Mursalat

Aya : 30

ٱنطَلِقُوٓاْ إِلَىٰ ظِلّٖ ذِي ثَلَٰثِ شُعَبٖ

Ku tafi zuwa wata inuwa mai rassa uku



Sura: Suratul Mursalat

Aya : 31

لَّا ظَلِيلٖ وَلَا يُغۡنِي مِنَ ٱللَّهَبِ

Ba mai ba da inuwa ba kuma ba mai karewa daga harshen wuta ba



Sura: Suratul Mursalat

Aya : 32

إِنَّهَا تَرۡمِي بِشَرَرٖ كَٱلۡقَصۡرِ

Haqiqa ita tana jefa tartsatsi kamar qaton gini



Sura: Suratul Mursalat

Aya : 33

كَأَنَّهُۥ جِمَٰلَتٞ صُفۡرٞ

Kai ka ce su raquma ne baqaqe



Sura: Suratul Mursalat

Aya : 34

وَيۡلٞ يَوۡمَئِذٖ لِّلۡمُكَذِّبِينَ

Tsananin azaba ya tabbata a wannan ranar ga masu qaryatawa



Sura: Suratul Mursalat

Aya : 35

هَٰذَا يَوۡمُ لَا يَنطِقُونَ

Wannan ita ce ranar da ba sa magana