Sura: Suratul Muddassir

Aya : 17

سَأُرۡهِقُهُۥ صَعُودًا

Ba da daxewa ba zan xora masa (azaba) mai matsananciyar wahala



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 18

إِنَّهُۥ فَكَّرَ وَقَدَّرَ

Lalle shi ya yi tunani, ya kuma auna (a ransa)



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 19

فَقُتِلَ كَيۡفَ قَدَّرَ

Sai aka la’ane shi, yaya ya yi irin wannan awon?



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 20

ثُمَّ قُتِلَ كَيۡفَ قَدَّرَ

Sannan aka kuma la’antar sa, yaya ya yi wannan awon?



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 21

ثُمَّ نَظَرَ

Sannan ya yi nazari



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 22

ثُمَّ عَبَسَ وَبَسَرَ

Sannan ya xaure fuska, ya kuma murtuke



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 23

ثُمَّ أَدۡبَرَ وَٱسۡتَكۡبَرَ

Sannan ya ba da baya (daga imani) ya kuma yi girman kai



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 24

فَقَالَ إِنۡ هَٰذَآ إِلَّا سِحۡرٞ يُؤۡثَرُ

Sai ya ce: “Wannan (Alqur’ani) ba komai ba ne sai sihiri da aka samo (daga wasu)



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 25

إِنۡ هَٰذَآ إِلَّا قَوۡلُ ٱلۡبَشَرِ

“Wannan ba komai ba ne sai magana irin ta mutane.”



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 26

سَأُصۡلِيهِ سَقَرَ

(Allah ya ce): Da sannu zan shigar da shi (wutar) Saqara



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 27

وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا سَقَرُ

Me ya sanar da kai abin da ake ce wa Saqara?



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 28

لَا تُبۡقِي وَلَا تَذَرُ

Ba ta ragewa kuma ba ta barin (komai)



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 29

لَوَّاحَةٞ لِّلۡبَشَرِ

Mai xaxxaye fata ce



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 30

عَلَيۡهَا تِسۡعَةَ عَشَرَ

Akwai (mala’iku) goma sha tara suna tsaron ta



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 31

وَمَا جَعَلۡنَآ أَصۡحَٰبَ ٱلنَّارِ إِلَّا مَلَـٰٓئِكَةٗۖ وَمَا جَعَلۡنَا عِدَّتَهُمۡ إِلَّا فِتۡنَةٗ لِّلَّذِينَ كَفَرُواْ لِيَسۡتَيۡقِنَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ وَيَزۡدَادَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ إِيمَٰنٗا وَلَا يَرۡتَابَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ وَٱلۡمُؤۡمِنُونَ وَلِيَقُولَ ٱلَّذِينَ فِي قُلُوبِهِم مَّرَضٞ وَٱلۡكَٰفِرُونَ مَاذَآ أَرَادَ ٱللَّهُ بِهَٰذَا مَثَلٗاۚ كَذَٰلِكَ يُضِلُّ ٱللَّهُ مَن يَشَآءُ وَيَهۡدِي مَن يَشَآءُۚ وَمَا يَعۡلَمُ جُنُودَ رَبِّكَ إِلَّا هُوَۚ وَمَا هِيَ إِلَّا ذِكۡرَىٰ لِلۡبَشَرِ

Ba Mu kuwa sanya masu tsaron wutar ba sai mala’iku, ba Mu kuma sanya adadinsu ba sai don fitina ga waxanda suka kafirta, don kuma waxanda aka bai wa littafi su sami yaqini, waxanda kuma suka yi imani su qara imani, waxanda aka bai wa littafi da muminai kuma kada su yi tababa, don kuma waxanda suke da raunin imani a zukatansu da kuma kafirai su ce: “Me Allah Yake nufi da yin misali da wannan (adadin)?” Kamar haka Allah Yake vatar da wanda Ya ga dama, Yake kuma shiryar da wanda Ya ga dama. Ba kuma wanda ya san (yawan) rundunar Ubangijinka sai Shi. Ita (Saqara) kuma ba wata abu ba ce face wa’azi ga mutane



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 32

كَلَّا وَٱلۡقَمَرِ

A’a. Na rantse da wata



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 33

وَٱلَّيۡلِ إِذۡ أَدۡبَرَ

Da kuma dare idan ya ba da baya



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 34

وَٱلصُّبۡحِ إِذَآ أَسۡفَرَ

Da kuma asuba idan ta bayyana (da haskenta)



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 35

إِنَّهَا لَإِحۡدَى ٱلۡكُبَرِ

Lalle ita (Saqara) tana xaya daga manya-manyan (bala’o’i)



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 36

نَذِيرٗا لِّلۡبَشَرِ

Gargaxi ce ga mutane



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 37

لِمَن شَآءَ مِنكُمۡ أَن يَتَقَدَّمَ أَوۡ يَتَأَخَّرَ

Ga wanda ya ga dama daga cikinku, ya ci gaba ko ya ci baya



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 38

كُلُّ نَفۡسِۭ بِمَا كَسَبَتۡ رَهِينَةٌ

Kowane rai jingina ne ga abin da ya tsuwurwurta[1]


1- Watau jingina ne ga ayyukansu, ko dai su hallakar da shi ko su kuvutar da shi, su ‘yanta shi.


Sura: Suratul Muddassir

Aya : 39

إِلَّآ أَصۡحَٰبَ ٱلۡيَمِينِ

Sai dai ga ma’abota dama[1]


1- Watau waxanda za su karvi littattafan ayyukansu ta hannayensu na dama.


Sura: Suratul Muddassir

Aya : 40

فِي جَنَّـٰتٖ يَتَسَآءَلُونَ

(Su kam suna) cikin gidajen Aljanna suna tambayar juna



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 41

عَنِ ٱلۡمُجۡرِمِينَ

Game da manyan masu laifuka



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 42

مَا سَلَكَكُمۡ فِي سَقَرَ

(Suna cewa): “Me ya shigar da ku cikin Saqara?”



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 43

قَالُواْ لَمۡ نَكُ مِنَ ٱلۡمُصَلِّينَ

Suka ce: “Ba mu zama daga cikin masallata ba



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 44

وَلَمۡ نَكُ نُطۡعِمُ ٱلۡمِسۡكِينَ

“Kuma ba mu kasance muna ciyar da miskini ba



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 45

وَكُنَّا نَخُوضُ مَعَ ٱلۡخَآئِضِينَ

“Mun kuma kasance muna kutsawa (cikin varna)[1] tare da masu kutsawa


1- Watau suna faxar qarerayi game da Annabi () da Alqur’ani.


Sura: Suratul Muddassir

Aya : 46

وَكُنَّا نُكَذِّبُ بِيَوۡمِ ٱلدِّينِ

“Kuma mun kasance muna qaryata ranar sakamako