Sura: Suratu Sad

Aya : 63

أَتَّخَذۡنَٰهُمۡ سِخۡرِيًّا أَمۡ زَاغَتۡ عَنۡهُمُ ٱلۡأَبۡصَٰرُ

“Shin mun xauke su ne ababen yi wa ba’a (a duniya), ko kuwa idanuwanmu ne suka bauxe ba sa hango su?”



Sura: Suratu Sad

Aya : 64

إِنَّ ذَٰلِكَ لَحَقّٞ تَخَاصُمُ أَهۡلِ ٱلنَّارِ

“Shin mun xauke su ne ababen yi wa ba’a (a duniya), ko kuwa idanuwanmu ne suka bauxe ba sa hango su?”



Sura: Suratu Sad

Aya : 65

قُلۡ إِنَّمَآ أَنَا۠ مُنذِرٞۖ وَمَا مِنۡ إِلَٰهٍ إِلَّا ٱللَّهُ ٱلۡوَٰحِدُ ٱلۡقَهَّارُ

Ka ce: “Ni dai mai gargaxi ne kawai; kuma babu wani abin bauta wa da gaskiya sai Allah Xaya, Mai rinjaye



Sura: Suratu Sad

Aya : 66

رَبُّ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا بَيۡنَهُمَا ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡغَفَّـٰرُ

“Ubangijin sammai da qasa da abin da yake tsakaninsu, Mabuwayi, Mai gafara.”



Sura: Suratu Sad

Aya : 67

قُلۡ هُوَ نَبَؤٌاْ عَظِيمٌ

Ka ce: “Shi (wannan Alqur’ani) labari ne mai girma



Sura: Suratu Sad

Aya : 68

أَنتُمۡ عَنۡهُ مُعۡرِضُونَ

“Da kuke bijire masa



Sura: Suratu Sad

Aya : 69

مَا كَانَ لِيَ مِنۡ عِلۡمِۭ بِٱلۡمَلَإِ ٱلۡأَعۡلَىٰٓ إِذۡ يَخۡتَصِمُونَ

“Ban zama na san wani abu ba dangane da mala’iku masu daraja lokacin da suke yin muhawara (game da halittar Adamu)



Sura: Suratu Sad

Aya : 70

إِن يُوحَىٰٓ إِلَيَّ إِلَّآ أَنَّمَآ أَنَا۠ نَذِيرٞ مُّبِينٌ

“Ba wani wahayi da aka yiwo min sai kawai cewa ni mai gargaxi ne mai bayyanawa.”



Sura: Suratu Sad

Aya : 71

إِذۡ قَالَ رَبُّكَ لِلۡمَلَـٰٓئِكَةِ إِنِّي خَٰلِقُۢ بَشَرٗا مِّن طِينٖ

(Ka tuna) lokacin da Ubangijinka Ya ce da mala’iku: “Lalle Ni zan halicci wani mutum daga tavo



Sura: Suratu Sad

Aya : 72

فَإِذَا سَوَّيۡتُهُۥ وَنَفَخۡتُ فِيهِ مِن رُّوحِي فَقَعُواْ لَهُۥ سَٰجِدِينَ

“To idan Na daidaita shi Na kuma busa masa ruhina, sai ku faxi kuna masu yi masa sujjada.”



Sura: Suratu Sad

Aya : 73

فَسَجَدَ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ كُلُّهُمۡ أَجۡمَعُونَ

Sai mala’iku dukkaninsu gaba xaya suka yi sujjada



Sura: Suratu Sad

Aya : 74

إِلَّآ إِبۡلِيسَ ٱسۡتَكۡبَرَ وَكَانَ مِنَ ٱلۡكَٰفِرِينَ

Sai Iblisa da ya yi girman kai ya kuma zama cikin kafirai



Sura: Suratu Sad

Aya : 75

قَالَ يَـٰٓإِبۡلِيسُ مَا مَنَعَكَ أَن تَسۡجُدَ لِمَا خَلَقۡتُ بِيَدَيَّۖ أَسۡتَكۡبَرۡتَ أَمۡ كُنتَ مِنَ ٱلۡعَالِينَ

(Allah) Ya ce: “Ya kai Iblisa, me ya hana ka yin sujjada ga abin da Na halitta da hannayena biyu? Ka yi girman kai ne, ko kuwa da man can ka kasance daga masu nuna isa?”



Sura: Suratu Sad

Aya : 76

قَالَ أَنَا۠ خَيۡرٞ مِّنۡهُ خَلَقۡتَنِي مِن نَّارٖ وَخَلَقۡتَهُۥ مِن طِينٖ

Sai ya ce: “Ni ai na fi shi; (domin) Ka halicce ni ne daga wuta, (shi) kuma Ka halicce shi daga tavo.”



Sura: Suratu Sad

Aya : 77

قَالَ فَٱخۡرُجۡ مِنۡهَا فَإِنَّكَ رَجِيمٞ

(Sai Allah) Ya ce (da shi): “To ka fice daga cikinta (wato Aljanna) saboda kai lalle korarre ne (daga rahama)



Sura: Suratu Sad

Aya : 78

وَإِنَّ عَلَيۡكَ لَعۡنَتِيٓ إِلَىٰ يَوۡمِ ٱلدِّينِ

“Kuma lalle la’antata tabbas ta hau kanka har zuwa ranar alqiyama.”



Sura: Suratu Sad

Aya : 79

قَالَ رَبِّ فَأَنظِرۡنِيٓ إِلَىٰ يَوۡمِ يُبۡعَثُونَ

(Sai Iblisa) ya ce: “Ya Ubangijina, Ka saurara min har zuwa ranar da za a tashe su.”



Sura: Suratu Sad

Aya : 80

قَالَ فَإِنَّكَ مِنَ ٱلۡمُنظَرِينَ

(Sai Allah) Ya ce: “To lalle kana cikin waxanda za a saurara wa



Sura: Suratu Sad

Aya : 81

إِلَىٰ يَوۡمِ ٱلۡوَقۡتِ ٱلۡمَعۡلُومِ

“Har zuwa ranar lokaci sananne.”



Sura: Suratu Sad

Aya : 82

قَالَ فَبِعِزَّتِكَ لَأُغۡوِيَنَّهُمۡ أَجۡمَعِينَ

Sai ya ce: “To na rantse da girmanka tabbas zan vatar da su baki xaya



Sura: Suratu Sad

Aya : 83

إِلَّا عِبَادَكَ مِنۡهُمُ ٱلۡمُخۡلَصِينَ

“Sai dai bayinka waxanda aka tsarkake daga cikinsu.”



Sura: Suratu Sad

Aya : 84

قَالَ فَٱلۡحَقُّ وَٱلۡحَقَّ أَقُولُ

(Allah) Ya ce: “Gaskiya (daga gare Ni take), kuma gaskiyar kawai Nake faxa!



Sura: Suratu Sad

Aya : 85

لَأَمۡلَأَنَّ جَهَنَّمَ مِنكَ وَمِمَّن تَبِعَكَ مِنۡهُمۡ أَجۡمَعِينَ

“Tabbas zan cika Jahannama da kai da kuma waxanda suka bi ka baki xaya.”



Sura: Suratu Sad

Aya : 86

قُلۡ مَآ أَسۡـَٔلُكُمۡ عَلَيۡهِ مِنۡ أَجۡرٖ وَمَآ أَنَا۠ مِنَ ٱلۡمُتَكَلِّفِينَ

Ka faxa (musu): “Babu wani lada da nake tambayar ku game da shi, (wato isar da aike), kuma ni ba na cikin masu matsa wa kai (don in qago wani sabon saqo)



Sura: Suratu Sad

Aya : 87

إِنۡ هُوَ إِلَّا ذِكۡرٞ لِّلۡعَٰلَمِينَ

“Shi ba wani abu ba ne in ban da tunatarwa ga talikai



Sura: Suratu Sad

Aya : 88

وَلَتَعۡلَمُنَّ نَبَأَهُۥ بَعۡدَ حِينِۭ

“Kuma tabbas za ku san gaskiyar labarinsa (watau Alqur’ani) bayan wani xan lokaci.”



Sura: Suratuz Zumar

Aya : 1

تَنزِيلُ ٱلۡكِتَٰبِ مِنَ ٱللَّهِ ٱلۡعَزِيزِ ٱلۡحَكِيمِ

Saukar Littafi daga Allah ne Mabuwayi, Mai hikima



Sura: Suratuz Zumar

Aya : 2

إِنَّآ أَنزَلۡنَآ إِلَيۡكَ ٱلۡكِتَٰبَ بِٱلۡحَقِّ فَٱعۡبُدِ ٱللَّهَ مُخۡلِصٗا لَّهُ ٱلدِّينَ

Lalle Mu Muka saukar maka Littafi da gaskiya, to ka bauta wa Allah kana mai tsantsanta addini a gare Shi



Sura: Suratuz Zumar

Aya : 3

أَلَا لِلَّهِ ٱلدِّينُ ٱلۡخَالِصُۚ وَٱلَّذِينَ ٱتَّخَذُواْ مِن دُونِهِۦٓ أَوۡلِيَآءَ مَا نَعۡبُدُهُمۡ إِلَّا لِيُقَرِّبُونَآ إِلَى ٱللَّهِ زُلۡفَىٰٓ إِنَّ ٱللَّهَ يَحۡكُمُ بَيۡنَهُمۡ فِي مَا هُمۡ فِيهِ يَخۡتَلِفُونَۗ إِنَّ ٱللَّهَ لَا يَهۡدِي مَنۡ هُوَ كَٰذِبٞ كَفَّارٞ

Ku saurara! Tsantsan addini na Allah ne[1]. Waxanda kuwa suka riqi wasu majivinta al’amari ba Shi ba (suna cewa): “Ba ma bauta musu sai kawai don su kusanta mu ga Allah.” Lalle Allah zai yi hukunci a tsakaninsu game da abin da suke sassavawa a cikinsa. Lalle Allah ba Ya shiryar da wanda yake maqaryaci, mai yawan kafirci


1- Watau addinin kaxaita Allah da guje wa shirka.


Sura: Suratuz Zumar

Aya : 4

لَّوۡ أَرَادَ ٱللَّهُ أَن يَتَّخِذَ وَلَدٗا لَّٱصۡطَفَىٰ مِمَّا يَخۡلُقُ مَا يَشَآءُۚ سُبۡحَٰنَهُۥۖ هُوَ ٱللَّهُ ٱلۡوَٰحِدُ ٱلۡقَهَّارُ

Da Allah Ya yi nufin Ya riqi xa, da sai Ya zavi wanda Ya ga dama daga abubuwan da Yake halitta. Tsarki ya tabbata a gare Shi. Shi ne Xaya, Mai rinjaye