Sura: Suratu Maryam

Aya : 85

يَوۡمَ نَحۡشُرُ ٱلۡمُتَّقِينَ إِلَى ٱلرَّحۡمَٰنِ وَفۡدٗا

Ranar da za Mu tayar da masu taqawa zuwa ga (Allah) Mai rahama a matsayin manyan baqi



Sura: Suratu Maryam

Aya : 86

وَنَسُوقُ ٱلۡمُجۡرِمِينَ إِلَىٰ جَهَنَّمَ وِرۡدٗا

Mu kuma kora kafirai zuwa Jahannama cikin tsananin qishirwa



Sura: Suratu Maryam

Aya : 87

لَّا يَمۡلِكُونَ ٱلشَّفَٰعَةَ إِلَّا مَنِ ٱتَّخَذَ عِندَ ٱلرَّحۡمَٰنِ عَهۡدٗا

Ba wani mai ikon yin ceto sai wanda yake da alqawari a wurin (Allah) Mai rahama[1]


1- Watau ya riqe alqawarin da ya yi na imani da Allah da manzanninsa.


Sura: Suratu Maryam

Aya : 88

وَقَالُواْ ٱتَّخَذَ ٱلرَّحۡمَٰنُ وَلَدٗا

Suka kuma ce: “(Allah) Mai rahama (wai) yana da xa



Sura: Suratu Maryam

Aya : 89

لَّقَدۡ جِئۡتُمۡ شَيۡـًٔا إِدّٗا

Haqiqa kun zo da babban abu (marar daxin ji)



Sura: Suratu Maryam

Aya : 90

تَكَادُ ٱلسَّمَٰوَٰتُ يَتَفَطَّرۡنَ مِنۡهُ وَتَنشَقُّ ٱلۡأَرۡضُ وَتَخِرُّ ٱلۡجِبَالُ هَدًّا

Sama ta kusa ta kece saboda shi (mummunan furucin), qasa kuma ta tsage, duwatsu kuma su zube su yi rugu-rugu



Sura: Suratu Maryam

Aya : 91

أَن دَعَوۡاْ لِلرَّحۡمَٰنِ وَلَدٗا

Saboda sun yi da’awar Allah Yana da xa!



Sura: Suratu Maryam

Aya : 92

وَمَا يَنۢبَغِي لِلرَّحۡمَٰنِ أَن يَتَّخِذَ وَلَدًا

Bai kuwa dace da (Allah) Mai rahama Ya zama Yana da xa ba



Sura: Suratu Maryam

Aya : 93

إِن كُلُّ مَن فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ إِلَّآ ءَاتِي ٱلرَّحۡمَٰنِ عَبۡدٗا

Ba wani abu da yake cikin sammai da qasa face ya zo wa (Allah) Mai rahama a matsayin bawa



Sura: Suratu Maryam

Aya : 94

لَّقَدۡ أَحۡصَىٰهُمۡ وَعَدَّهُمۡ عَدّٗا

Lalle Ya kiyaye da su Ya kuma qididdige su sosai



Sura: Suratu Maryam

Aya : 95

وَكُلُّهُمۡ ءَاتِيهِ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِ فَرۡدًا

Kuma dukkansu kowa zai zo masa a ranar alqiyama shi kaxai



Sura: Suratu Maryam

Aya : 96

إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ سَيَجۡعَلُ لَهُمُ ٱلرَّحۡمَٰنُ وُدّٗا

Lalle waxanda suka yi imani suka kuma yi aiki na gari, to (Allah) Mai rahama zai sanya musu qauna[1]


1- Watau zanya farin jininsu a zukatan masoyansa a sama da qasa. Shi ma kuma zai qaunace su.


Sura: Suratu Maryam

Aya : 97

فَإِنَّمَا يَسَّرۡنَٰهُ بِلِسَانِكَ لِتُبَشِّرَ بِهِ ٱلۡمُتَّقِينَ وَتُنذِرَ بِهِۦ قَوۡمٗا لُّدّٗا

To Mun dai sauqaqe shi (Alqur’ani) da harshenka ne don kawai ka yi wa masu taqawa albishir da shi, ka kuma gargaxi mutane masu tsananin jayayya da shi



Sura: Suratu Maryam

Aya : 98

وَكَمۡ أَهۡلَكۡنَا قَبۡلَهُم مِّن قَرۡنٍ هَلۡ تُحِسُّ مِنۡهُم مِّنۡ أَحَدٍ أَوۡ تَسۡمَعُ لَهُمۡ رِكۡزَۢا

Al’umma nawa Muka hallaka a gabaninsu, shin kana jin xuriyar wani daga cikinsu, ko kuwa kana jin ‘yar muryarsu?



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 1

طه

Xa Ha[1]


1- Duba Suratul Baqara, aya ta 1, hashiya ta 8.


Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 2

مَآ أَنزَلۡنَا عَلَيۡكَ ٱلۡقُرۡءَانَ لِتَشۡقَىٰٓ

Ba Mu saukar maka da Alqur’ani don ka wahala ba



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 3

إِلَّا تَذۡكِرَةٗ لِّمَن يَخۡشَىٰ

Sai don wa’azi ga wanda zai ji tsoron (haxuwa da Allah)



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 4

تَنزِيلٗا مِّمَّنۡ خَلَقَ ٱلۡأَرۡضَ وَٱلسَّمَٰوَٰتِ ٱلۡعُلَى

Saukakke ne daga wanda Ya halicci qasa da sammai masu xaukaka



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 5

ٱلرَّحۡمَٰنُ عَلَى ٱلۡعَرۡشِ ٱسۡتَوَىٰ

(Allah) Mai rahama, Ya daidaita a kan Al’arshi[1]


1- Duba Suratul A’arafi, aya ta 54, hashiya ta 126.


Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 6

لَهُۥ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَا فِي ٱلۡأَرۡضِ وَمَا بَيۡنَهُمَا وَمَا تَحۡتَ ٱلثَّرَىٰ

Abin da yake sammai da qasa, da abin da yake tsakaninsu da kuma abin da yake qarqashin qasa, (duka) nasa ne



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 7

وَإِن تَجۡهَرۡ بِٱلۡقَوۡلِ فَإِنَّهُۥ يَعۡلَمُ ٱلسِّرَّ وَأَخۡفَى

Idan kuma ka xaga murya da furuci to lalle Shi Yana sane da sirri da abin da ya fi (sirri) vuya



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 8

ٱللَّهُ لَآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَۖ لَهُ ٱلۡأَسۡمَآءُ ٱلۡحُسۡنَىٰ

Allah (Shi ne wanda) babu wani abin bauta da gaskiya sai Shi; Yana da sunaye mafiya kyau



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 9

وَهَلۡ أَتَىٰكَ حَدِيثُ مُوسَىٰٓ

Shin kuwa labarin Musa ya zo maka?



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 10

إِذۡ رَءَا نَارٗا فَقَالَ لِأَهۡلِهِ ٱمۡكُثُوٓاْ إِنِّيٓ ءَانَسۡتُ نَارٗا لَّعَلِّيٓ ءَاتِيكُم مِّنۡهَا بِقَبَسٍ أَوۡ أَجِدُ عَلَى ٱلنَّارِ هُدٗى

Lokacin da ya gano wuta sai ya ce da iyalinsa: “Ku zauna (a nan), lalle ni fa na hangi wuta, (zan je) ko na zo muku da garwashinta ko kuma in sami mai nuna mini (hanya) a wurin wutar.”



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 11

فَلَمَّآ أَتَىٰهَا نُودِيَ يَٰمُوسَىٰٓ

To lokacin da ya zo wurinta (wato wutar), sai aka kira shi (cewa): “Ya Musa



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 12

إِنِّيٓ أَنَا۠ رَبُّكَ فَٱخۡلَعۡ نَعۡلَيۡكَ إِنَّكَ بِٱلۡوَادِ ٱلۡمُقَدَّسِ طُوٗى

“Lalle Ni, Ni ne fa Ubangijinka, sai ka tuve takalmanka; lalle kana a tsarkakakken kwarin Xuwa ne



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 13

وَأَنَا ٱخۡتَرۡتُكَ فَٱسۡتَمِعۡ لِمَا يُوحَىٰٓ

“Kuma Ni Na zave ka (da manzanci), sai ka ji abin da za a yiwo ma wahayi (da shi)



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 14

إِنَّنِيٓ أَنَا ٱللَّهُ لَآ إِلَٰهَ إِلَّآ أَنَا۠ فَٱعۡبُدۡنِي وَأَقِمِ ٱلصَّلَوٰةَ لِذِكۡرِيٓ

“Lalle Ni, Ni ne Allah, babu wani abin bauta sai Ni, to ka bauta mini, kuma ka tsai da salla don tuna Ni



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 15

إِنَّ ٱلسَّاعَةَ ءَاتِيَةٌ أَكَادُ أُخۡفِيهَا لِتُجۡزَىٰ كُلُّ نَفۡسِۭ بِمَا تَسۡعَىٰ

“Lalle alqiyama za ta zo, ina nufin voye ta ne don a saka wa kowanne rai da irin abin da yake aikatawa



Sura: Suratu Xa Ha

Aya : 16

فَلَا يَصُدَّنَّكَ عَنۡهَا مَن لَّا يُؤۡمِنُ بِهَا وَٱتَّبَعَ هَوَىٰهُ فَتَرۡدَىٰ

“To kada wanda bai yi imani da ita ba ya kuma bi son ransa ya hana ka gaskata ta, sai ka hallaka