وَخَلَقَ ٱلۡجَآنَّ مِن مَّارِجٖ مِّن نَّارٖ
Ya kuma halicci aljani daga harshen wuta
فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?
رَبُّ ٱلۡمَشۡرِقَيۡنِ وَرَبُّ ٱلۡمَغۡرِبَيۡنِ
Ubangijin mahudar rana biyu da mafaxarta biyu[1]
1- Watau a lokacin sanyi da kuma lokacin zafi.
فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?
مَرَجَ ٱلۡبَحۡرَيۡنِ يَلۡتَقِيَانِ
Ya gudanar da koguna guda biyu suna haxuwa (da juna)
بَيۡنَهُمَا بَرۡزَخٞ لَّا يَبۡغِيَانِ
A tsakaninsu (kuma) akwai wani shamaki da ya hana su shiga juna
فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?
يَخۡرُجُ مِنۡهُمَا ٱللُّؤۡلُؤُ وَٱلۡمَرۡجَانُ
Lu’ulu’u da murjani suna fita daga cikinsu
فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?
وَلَهُ ٱلۡجَوَارِ ٱلۡمُنشَـَٔاتُ فِي ٱلۡبَحۡرِ كَٱلۡأَعۡلَٰمِ
Jiragen ruwa kuma da aka yi su suna gudu a cikin kogi kamar manya-manyan duwatsu nasa ne
فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?
كُلُّ مَنۡ عَلَيۡهَا فَانٖ
Dukkan wanda yake kanta (qasar) qararre ne
وَيَبۡقَىٰ وَجۡهُ رَبِّكَ ذُو ٱلۡجَلَٰلِ وَٱلۡإِكۡرَامِ
Fuskar Ubangijinka kuwa Ma’abocin girma da karamci ne kawai take wanzuwa
فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?
يَسۡـَٔلُهُۥ مَن فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ كُلَّ يَوۡمٍ هُوَ فِي شَأۡنٖ
Duk wanda yake cikin sammai da qasa yana roqon Sa. Kowane lokacin Shi a cikin wani sha’ani yake
فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?
سَنَفۡرُغُ لَكُمۡ أَيُّهَ ٱلثَّقَلَانِ
Ba da daxewa ba za Mu dawo kanku ya ku mutane da aljannu
فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?
يَٰمَعۡشَرَ ٱلۡجِنِّ وَٱلۡإِنسِ إِنِ ٱسۡتَطَعۡتُمۡ أَن تَنفُذُواْ مِنۡ أَقۡطَارِ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ فَٱنفُذُواْۚ لَا تَنفُذُونَ إِلَّا بِسُلۡطَٰنٖ
Ya ku jama’ar aljannu da mutane, idan kun sami ikon ficewa daga cikin sassan sammai da qasa to ku fice. Ba za ku fice ba sai da samun wani qarfi[1]
1- Watau ba za su kuvuce wa Allah ba sai idan suna da wata hujja ko wani qarfi, wanda kuma su ma sun tabbata ba su da shi.
فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?
يُرۡسَلُ عَلَيۡكُمَا شُوَاظٞ مِّن نَّارٖ وَنُحَاسٞ فَلَا تَنتَصِرَانِ
Za a aiko muku (ku mutane da aljannu) da balbalin wuta da kuma hayaqi, saboda haka ba za ku iya kare kanku (daga gare shi) ba
فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?
فَإِذَا ٱنشَقَّتِ ٱلسَّمَآءُ فَكَانَتۡ وَرۡدَةٗ كَٱلدِّهَانِ
Sannan idan sama ta kekkece ta zama jajir kamar jar fata[1]
1- Watau saboda an gusar da hasken taurarin cikinta gaba xaya.
فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?
فَيَوۡمَئِذٖ لَّا يُسۡـَٔلُ عَن ذَنۢبِهِۦٓ إِنسٞ وَلَا جَآنّٞ
Sannan a wannan rana ba a tambayar mutum ko aljan laifinsa
فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?
يُعۡرَفُ ٱلۡمُجۡرِمُونَ بِسِيمَٰهُمۡ فَيُؤۡخَذُ بِٱلنَّوَٰصِي وَٱلۡأَقۡدَامِ
Ana gane manyan masu laifi da alamominsu[1], sai a kama su ta makwarkwaxa da dugadugai
1- Saboda fuskokinsu za su yi baqi qirin, idanuwansu kuma za su yi jawur.
فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?
هَٰذِهِۦ جَهَنَّمُ ٱلَّتِي يُكَذِّبُ بِهَا ٱلۡمُجۡرِمُونَ
(Za a ce da su): Wannan ita ce Jahannamar da manyan masu laifi suke qaryatawa
يَطُوفُونَ بَيۡنَهَا وَبَيۡنَ حَمِيمٍ ءَانٖ
Za su riqa kai-kawo tsakaninta da tafasasshen ruwa mai tsananin zafi