Sura: Suratul Muddassir

Aya : 31

وَمَا جَعَلۡنَآ أَصۡحَٰبَ ٱلنَّارِ إِلَّا مَلَـٰٓئِكَةٗۖ وَمَا جَعَلۡنَا عِدَّتَهُمۡ إِلَّا فِتۡنَةٗ لِّلَّذِينَ كَفَرُواْ لِيَسۡتَيۡقِنَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ وَيَزۡدَادَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ إِيمَٰنٗا وَلَا يَرۡتَابَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ وَٱلۡمُؤۡمِنُونَ وَلِيَقُولَ ٱلَّذِينَ فِي قُلُوبِهِم مَّرَضٞ وَٱلۡكَٰفِرُونَ مَاذَآ أَرَادَ ٱللَّهُ بِهَٰذَا مَثَلٗاۚ كَذَٰلِكَ يُضِلُّ ٱللَّهُ مَن يَشَآءُ وَيَهۡدِي مَن يَشَآءُۚ وَمَا يَعۡلَمُ جُنُودَ رَبِّكَ إِلَّا هُوَۚ وَمَا هِيَ إِلَّا ذِكۡرَىٰ لِلۡبَشَرِ

Ba Mu kuwa sanya masu tsaron wutar ba sai mala’iku, ba Mu kuma sanya adadinsu ba sai don fitina ga waxanda suka kafirta, don kuma waxanda aka bai wa littafi su sami yaqini, waxanda kuma suka yi imani su qara imani, waxanda aka bai wa littafi da muminai kuma kada su yi tababa, don kuma waxanda suke da raunin imani a zukatansu da kuma kafirai su ce: “Me Allah Yake nufi da yin misali da wannan (adadin)?” Kamar haka Allah Yake vatar da wanda Ya ga dama, Yake kuma shiryar da wanda Ya ga dama. Ba kuma wanda ya san (yawan) rundunar Ubangijinka sai Shi. Ita (Saqara) kuma ba wata abu ba ce face wa’azi ga mutane



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 32

كَلَّا وَٱلۡقَمَرِ

A’a. Na rantse da wata



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 33

وَٱلَّيۡلِ إِذۡ أَدۡبَرَ

Da kuma dare idan ya ba da baya



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 34

وَٱلصُّبۡحِ إِذَآ أَسۡفَرَ

Da kuma asuba idan ta bayyana (da haskenta)



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 35

إِنَّهَا لَإِحۡدَى ٱلۡكُبَرِ

Lalle ita (Saqara) tana xaya daga manya-manyan (bala’o’i)



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 36

نَذِيرٗا لِّلۡبَشَرِ

Gargaxi ce ga mutane



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 37

لِمَن شَآءَ مِنكُمۡ أَن يَتَقَدَّمَ أَوۡ يَتَأَخَّرَ

Ga wanda ya ga dama daga cikinku, ya ci gaba ko ya ci baya



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 38

كُلُّ نَفۡسِۭ بِمَا كَسَبَتۡ رَهِينَةٌ

Kowane rai jingina ne ga abin da ya tsuwurwurta[1]


1- Watau jingina ne ga ayyukansu, ko dai su hallakar da shi ko su kuvutar da shi, su ‘yanta shi.


Sura: Suratul Muddassir

Aya : 39

إِلَّآ أَصۡحَٰبَ ٱلۡيَمِينِ

Sai dai ga ma’abota dama[1]


1- Watau waxanda za su karvi littattafan ayyukansu ta hannayensu na dama.


Sura: Suratul Muddassir

Aya : 40

فِي جَنَّـٰتٖ يَتَسَآءَلُونَ

(Su kam suna) cikin gidajen Aljanna suna tambayar juna



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 41

عَنِ ٱلۡمُجۡرِمِينَ

Game da manyan masu laifuka



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 42

مَا سَلَكَكُمۡ فِي سَقَرَ

(Suna cewa): “Me ya shigar da ku cikin Saqara?”



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 43

قَالُواْ لَمۡ نَكُ مِنَ ٱلۡمُصَلِّينَ

Suka ce: “Ba mu zama daga cikin masallata ba



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 44

وَلَمۡ نَكُ نُطۡعِمُ ٱلۡمِسۡكِينَ

“Kuma ba mu kasance muna ciyar da miskini ba



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 45

وَكُنَّا نَخُوضُ مَعَ ٱلۡخَآئِضِينَ

“Mun kuma kasance muna kutsawa (cikin varna)[1] tare da masu kutsawa


1- Watau suna faxar qarerayi game da Annabi () da Alqur’ani.


Sura: Suratul Muddassir

Aya : 46

وَكُنَّا نُكَذِّبُ بِيَوۡمِ ٱلدِّينِ

“Kuma mun kasance muna qaryata ranar sakamako



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 47

حَتَّىٰٓ أَتَىٰنَا ٱلۡيَقِينُ

“Har mutuwa ta zo mana.”



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 48

فَمَا تَنفَعُهُمۡ شَفَٰعَةُ ٱلشَّـٰفِعِينَ

Saboda haka ceton masu ceto ba zai amfane su ba



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 49

فَمَا لَهُمۡ عَنِ ٱلتَّذۡكِرَةِ مُعۡرِضِينَ

To me ya same su ne suke bijire wa wa’azi?



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 50

كَأَنَّهُمۡ حُمُرٞ مُّسۡتَنفِرَةٞ

Kai ka ce su jakunan jeji ne da aka firgitar



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 51

فَرَّتۡ مِن قَسۡوَرَةِۭ

Da suka guje wa zaki



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 52

بَلۡ يُرِيدُ كُلُّ ٱمۡرِيٕٖ مِّنۡهُمۡ أَن يُؤۡتَىٰ صُحُفٗا مُّنَشَّرَةٗ

A’a, kowane mutum daga cikinsu yana so ne a ba shi takardu buxaxxu[1] (kafin su bi Annabi)


1- Watau a ba shi buxaxxen littafi wanda zai ba shi labari cewa Annabi Muhammadu () Manzon Allah ne.


Sura: Suratul Muddassir

Aya : 53

كَلَّاۖ بَل لَّا يَخَافُونَ ٱلۡأٓخِرَةَ

Faufau! A’a, su dai ba sa tsoron ranar lahira ne



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 54

كَلَّآ إِنَّهُۥ تَذۡكِرَةٞ

Tabbas, lalle shi (Alqur’ani) wa’azi ne



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 55

فَمَن شَآءَ ذَكَرَهُۥ

To duk wanda ya ga dama sai ya wa’azantu



Sura: Suratul Muddassir

Aya : 56

وَمَا يَذۡكُرُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُۚ هُوَ أَهۡلُ ٱلتَّقۡوَىٰ وَأَهۡلُ ٱلۡمَغۡفِرَةِ

Ba sa kuma wa’azantuwa sai idan Allah Ya ga dama. Shi ne Ya cancanci taqawa, kuma Shi ne Ya cancanci yin gafara